< Irmiya 29 >
1 Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Dette er innholdet av det brev som profeten Jeremias sendte fra Jerusalem til de gjenlevende av de eldste blandt de bortførte og til prestene og profetene og hele det folk som Nebukadnesar hadde bortført fra Jerusalem til Babel,
2 (Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
efterat kong Jekonja og kongens mor og hoffmennene, Judas og Jerusalems høvdinger og tømmermennene og smedene hadde draget bort fra Jerusalem.
3 Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
Han sendte brevet med El'asa, Safans sønn, og Gemarja, Hilkias' sønn, som Judas konge Sedekias sendte til Babel, til Babels konge Nebukadnesar, og det lød således:
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud, til alle dem som jeg har ført bort fra Jerusalem til Babel:
5 “Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
Bygg hus og bo i dem, plant haver og et deres frukt!
6 Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
Ta eder hustruer og få sønner og døtre, og ta hustruer til eders sønner og gift bort eders døtre, så de kan få føde sønner og døtre; bli tallrike der, og bli ikke færre!
7 Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
Og søk den bys vel som jeg har bortført eder til, og bed for den til Herren! For når det går den vel, så går det eder vel.
8 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
For så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud: La ikke eders profeter, som er iblandt eder, og eders spåmenn dåre eder, og lytt heller ikke til de drømmer som I har!
9 Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
For falskelig profeterer de for eder i mitt navn; jeg har ikke sendt dem, sier Herren.
10 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
For så sier Herren: Når sytti år er gått til ende for Babel, vil jeg se til eder og opfylle for eder mitt gode ord, at jeg vil føre eder tilbake til dette sted.
11 Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
For jeg vet de tanker jeg tenker om eder, sier Herren, fredstanker og ikke tanker til ulykke, å gi eder fremtid og håp.
12 Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
Og I skal påkalle mig og gå avsted og bede til mig, og jeg vil høre på eder,
13 Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
og I skal søke mig, og I skal finne mig når I søker mig av hele eders hjerte.
14 Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
Jeg vil la mig finne av eder, sier Herren, og jeg vil gjøre ende på eders fangenskap og samle eder fra alle de folk og alle de steder som jeg har drevet eder bort til, sier Herren, og jeg vil føre eder tilbake til det sted som jeg førte eder bort fra.
15 Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
Dette skriver jeg fordi I sier: Herren har latt profeter fremstå for oss i Babel.
16 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
For så sier Herren om kongen som sitter på Davids trone, og om alt folket som bor i denne by, eders brødre, som ikke har draget ut med eder blandt de bortførte -
17 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
så sier Herren, hærskarenes Gud: Se, jeg sender sverd, hunger og pest iblandt dem og gjør med dem som en gjør med de dårlige fikener, som ikke kan etes, fordi de er så dårlige.
18 Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
Og jeg vil forfølge dem med sverd, hunger og pest, og jeg vil la dem bli mishandlet av alle jordens riker og gjøre dem til en forbannelse og en forferdelse, til spott og hån blandt alle de folkeslag som jeg driver dem bort til,
19 Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
fordi de ikke hørte på mine ord, sier Herren, da jeg sendte mine tjenere profetene til dem, tidlig og sent; men I vilde ikke høre, sier Herren.
20 Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
Men hør nu I Herrens ord, alle I bortførte som jeg har sendt fra Jerusalem til Babel!
21 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
Så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud, om Akab, Kolajas sønn, og om Sedekias, Ma'asejas sønn, som profeterer løgn for eder i hans navn: Se, jeg gir dem i Babels konge Nebukadnesars hånd, og han skal drepe dem for eders øine.
22 Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
Og fra dem skal alle Judas bortførte som er i Babel, hente en forbannelse og si: Herren gjøre med dig som med Sedekias og med Akab, som Babels konge stekte i ilden,
23 Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
fordi de gjorde en skjendig gjerning i Israel og drev hor med hverandres hustruer og talte løgnaktige ord i mitt navn, noget jeg ikke hadde befalt dem; og jeg vet det og er vidne, sier Herren.
24 Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
Og til nehelamitten Semaja skal du si:
25 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
Så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud: Du har sendt brev i ditt eget navn til alt folket i Jerusalem og til presten Sefanja, Ma'asejas sønn, og til alle prestene og sagt:
26 ‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
Herren har satt dig til prest i presten Jojadas sted, forat det skal være tilsynsmenn i Herrens hus over alle som er fra vettet og gir sig av med å profetere, så du kan legge dem i blokk og bånd.
27 To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
Hvorfor har du da ikke refset Jeremias fra Anatot, som gir sig av med å profetere for eder?
28 Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
For han har sendt brev til oss i Babel og sagt: Det vil vare lenge; bygg hus og bo i dem, plant haver og et deres frukt!
29 Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
Og presten Sefanja leste op dette brev for profeten Jeremias.
30 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Da kom Herrens ord til Jeremias, og det lød så:
31 “Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
Send bud til alle de bortførte og si: Så sier Herren om nehelamitten Semaja: Fordi Semaja har profetert for eder uten at jeg har sendt ham, og har fått eder til å sette eders lit til løgn,
32 ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”
derfor sier Herren så: Se, jeg hjemsøker nehelamitten Semaja og hans ætt; ingen av hans ætt skal få bo blandt dette folk, og han skal ikke få se det gode jeg gjør for mitt folk, sier Herren; for han har preket frafall fra Herren.