< Irmiya 29 >

1 Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Ma e baruwa mane janabi Jeremia ooro koa Jerusalem ne jodongo mane otony e dier jotwech kod ne jodolo, jonabi kod ji mamoko duto mane Nebukadneza notero e twech koa Jerusalem nyaka Babulon.
2 (Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
(Ma ne en bangʼ ka Ruoth Jehoyakin kod min ruoth, jotelo mag agola kod jotend Juda gi Jerusalem, jopecho gi jogoro osedhi e twech koa Jerusalem.)
3 Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
Nomiyo Elasa wuod Shafan kod Gemaria wuod Hilkia baruwa, jogo mane Zedekia ruodh Juda nooro Babulon ir Ruoth Nebukadneza. Kawacho niya:
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Ma e gima Jehova Nyasaye Maratego, ma Nyasach Israel, wacho ne jogo duto mane atero e twech koa Jerusalem nyaka Babulon:
5 “Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
“Geruru udi kendo udag kanyo; pidhuru puothe kendo ucham gik ma ginyago.
6 Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
Nyomburu mondo onywol yawuowi kod nyiri; yuduru mon ne yawuotu kendo uchiw nyiu mondo onyuom, magin bende ginywol yawuotgi kod nyigi mondo kwanu omedre kendo kik udog chien.
7 Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
Bende, dwaruru kwe kod mwandu mar dala maduongʼ ma aseterou e twech. Lamuru Jehova Nyasaye, ndalono nikech kodhi maber to un bende unudhi maber.”
8 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
Ee, ma e gima Jehova Nyasaye Maratego, ma Nyasach Israel, wacho: “Kik iwe jonabi kod joma neno wach e lek manie dieru wuondu. Kik uchik itu ne lek ma gileko nikech mano miyo gimedo leko.
9 Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
Gikoro miriambo gi nyinga. Ok aorogi,” Jehova Nyasaye owacho.
10 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: “Bangʼ ka usetieko higni piero abiriyo e Babulon, to anabi iru kendo achop singo mara mar ngʼwono mondo aduogu ka.”
11 Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
Nimar Jehova Nyasaye wacho niya, “Angʼeyo chenro ma an-go kodu. Chenro mar dhi maber to ok mar hinyou, chenro mar miyou geno kod ngima mabiro.
12 Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
Eka unuluonga mi anabi kendo ulama, to anawinju.
13 Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
Unudwara kendo unuyuda ka udwara gi chunyu duto.
14 Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
Ununwangʼa kendo anaduogu ka ua e twech. Anachoku ka ua e pinje duto kod kuonde ma asekeyoue kendo anaduogu kama ne uae ka aterou e twech,” Jehova Nyasaye owacho.
15 Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
Unyalo wacho niya, “Jehova Nyasaye osemiyowa jonabi ei Babulon,”
16 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
to ma e gima Jehova Nyasaye wacho kuom ruoth mobet e kom duongʼ mar Daudi kod jogo duto modongʼ e dala maduongʼni, jopinyu mane ok odhi kodu e twech;
17 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
adiera, ma e gima Jehova Nyasaye Maratego wacho: “Anaor ligangla, kech kod masira kuomgi kendo analokgi ka ngʼope maricho ma ok nyal cham.
18 Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
Analawgi gi ligangla, kech kod masira kendo anami gibed joma bwogo gwenge duto manie piny kendo gir kwongʼ kod bwok, gima ok onego mi luor kendo ma jaricho, e dier ogendini duto mane aseriembogie.”
19 Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
Jehova Nyasaye wacho niya, “Nimar pok giwinjo wechena, ma gin weche mane aoronegi kuom jotichna ma jonabi. To kata mana un joma ne oter e twech pok uwinja,” Jehova Nyasaye owacho.
20 Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
Emomiyo, winjuru wach Jehova Nyasaye, un joma ni e twech duto ma aseriembo koa Jerusalem nyaka Babulon.
21 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
Ma e gima Jehova Nyasaye Maratego, ma Nyasach Israel, wacho kuom Ahab wuod Kolaya kod Zedekia wuod Maseya, ma koronu miriambo e nyinga: “Anachiwgi ne Nebukadneza ruodh Babulon, kendo enoneg-gi e nyimu ka uneno.
22 Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
Nikech gin, joma ni e twech duto moa Juda man Babulon noti gi kwongʼni kawacho ni: ‘Mad Jehova Nyasaye timnu mana kaka notimone Zedekia kod Ahab, mane ruodh Babulon owangʼo e mach.’
23 Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
Nimar gisetimo gik mamono ei Israel; giseterore gi monde jobathgi kendo e nyinga gisewacho miriambo, mane ok anyisogi mondo giwachi. Angʼeye kendo an janeno kuom wachno,” Jehova Nyasaye owacho.
24 Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
Nyis Shemaya ja-Nehelam,
25 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
“Ma e gima Jehova Nyasaye Maratego ma Nyasach Israel, wacho: Ne ioro barupe e nyingi iwuon ne ji duto man Jerusalem, ne Zefania wuod Maseya jadolo, kendo ne jodolo mamoko duto. Ne iwachone Zefania ni,
26 ‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
‘Jehova Nyasaye oseyieri jadolo kar Jehoyada mondo ibed jarit od Jehova Nyasaye; omiyo koro ngʼato ma janeko mawuondore ni janabi onego itwe gi nyororo kod chuma molworo ngʼute.
27 To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
Marangʼo pod ok imako Jeremia moa Anathoth, ma ketore ni janabi e dieru?
28 Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
Oseoranwa wachni Babulon: Enobed kinde marabora. Emomiyo geruru udi kendo udagie eigi; pidhuru puothe kendo ucham gigo ma ginyago.’”
29 Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
Zefania jadolo, kata kamano, nosomo baruwani ne Jeremia janabi.
30 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Eka wach Jehova Nyasaye nobiro ne Jeremia ni,
31 “Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
“Or wachni ne joma ni e twech duto: ‘Ma e gima Jehova Nyasaye wacho kuom Shemaya ja-Nehelam: Nikech Shemaya osekoronu, kata obedo ni ne ok aore, kendo osemiyo uyie gi miriambo,
32 ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”
ma e gima Jehova Nyasaye wacho: Adier, anakum Shemaya ja-Nehelam kod gunde. Onge ngʼama nodongʼ kuom joge, kata neno gik mabeyo mabiro timo ne joga, nikech oselando mondo ji ongʼanyna. An Jehova Nyasaye ema awacho kamano.’”

< Irmiya 29 >