< Irmiya 29 >

1 Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
He cabu ol he Jerusalem lamkah tonghma Jeremiah loh vangsawn patong hlangrhuel taeng neh khosoih rhoek taeng neh, tonghma rhoek taeng neh, Nebukhanezar loh Jerusalem lamkah Babylon duela a poelyoe pilnam boeih taengah,
2 (Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
Manghai Jekoniah neh manghainu, Judah tildit mangpa rhoek neh Jerusalem rhoek, Jerusalem kah kutthai rhoek neh thidae rhoek a khuen phoeiah tah,
3 Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
Shaphan capa Elasah neh Hilkiah capa Gemariah kut dongah a pat. Amih rhoi te Babylon manghai Nebukhanezar taengkah Judah manghai Zedekiah taengah Babylon la a tueih tih,
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Israel Pathen caempuei BOEIPA loh he ni a. thui. vangsawn boeih te Jerusalem lamloh Babylon la ka poelyoe coeng.
5 “Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
Im thoh uh lamtah khosa uh, dum tue uh lamtah a thaih te ca uh.
6 Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
Yuu lo uh lamtah canu neh capa cun uh. Na capa ham khaw yuu loh pah lamtah na canu te a va taengah pae. Te daengah ni canu neh capa a sak uh vetih a ping uh pahoi neh na muei uh pawt eh.
7 Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
Te lam te nangmih kam poelyoe akhaw khopuei kah ngaimongnah mah toem uh. Te ham te BOEIPA taengah thangthui uh lamtah a ngaimongnah dongah nangmih ham ngaimongnah om bitni.
8 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
Israel Pathen caempuei BOEIPA loh he ni a. thui. Nangmih khui kah na tonghma rhoek neh nangmih taengkah bihma rhoek loh nangmih te n'rhaithi boel saeh. Na mang na man uh te khaw hnatung uh boeh.
9 Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
Amih te kan tueih pawt dae nangmih taengah tah kai ming neh a honghi lam ni a tonghma uh. He tah BOEIPA kah olphong ni.
10 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
He tah BOEIPA long ni a thui. Ka ka dongkah he Babylon ham soep ni. Kum sawmrhih vaengah nangmih kang hip vetih he hmuen la nangmih te mael puei ham ka ol then he nangmih soah ka thoh ni.
11 Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
Nangmih ham ka poek, kopoek te khaw ka ming ngawn. He tah BOEIPA kah olphong coeng ni. Ngaimong kopoek neh nangmih taengah hmailong ngaiuepnah paek ham te yoethaenah ham moenih.
12 Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
Te vaengah kai he nan khue uh vetih na pongpa uh ni. Kai taengah na thangthui uh vaengah nangmih taengkah ka hnatun ni.
13 Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
Kai nan tlap uh vaengah nan hmuh uh bitni. Te vaengah na thinko boeih neh kai nan toem uh mako ne.
14 Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
Nangmih te kan hmuh bitni. He tah BOEIPA kah olphong coeng ni. Nangmih khuikah thongtla, thongtla te ka mael sak vetih namtom boeih lamkah neh nangmih kang heh nah hmuen boeih lamloh nangmih te kan coi. He tah BOEIPA kah olphong ni. Nangmih kam poelyoe hmuen lamloh nangmih te kam mael puei ni.
15 Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
'BOEIPA loh mamih ham Babylon ah tonghma a phoe,’ na ti uh.
16 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
Tedae BOEIPA loh David kah ngolkhoel dongah aka ngol manghai kawng neh he khopuei kah khosa pilnam boeih kah a kawng, nangmih neh vangsawn la aka cet pawh na manuca kawng ni a thui tangkhuet.
17 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
Caempuei BOEIPA loh he ni a. thui. Kai loh amih taengah cunghang, khokha neh duektahaw khaw ka tueih coeng ke. Amih te thaibu thaihuk bangla ka khueh vetih a thaenah te ca uh thai mahpawh.
18 Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
Amih hnukah cunghang neh, khokha neh, duektahaw neh ka hloem vetih tonganah neh ngaihuetnah la, diklai ram boeih taengah thaephoeinah la, imsuep la, thuithetnah la, amih ka heh nah namtom boeih taengah kokhahnah la amih te ka khueh ni.
19 Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
Ka ol he a hnatun uh moenih te. He tah BOEIPA kah olphong ni. Amih taengah ka sal tonghma rhoek te kan tueih. A thoh neh kan tueih akhaw na hnatun uh moenih. He tah BOEIPA kah olphong ni.
20 Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
Te dongah Jerusalem lamloh Babylon la ka tueih nangmih vangsawn boeih loh BOEIPA ol he hnatun uh.
21 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
Israel Pathen caempuei BOEIPA loh Kolaiah capa Ahab neh Maaseiah capa Zedekiah kawng, kai ming neh nangmih taengah a honghi la aka tonghma rhoek he a thui. Amih te Babylon manghai Nebukhanezar kut dongah ka tloeng coeng tih nangmih mikhmuh ah amih te a ngawn ni.
22 Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
Amih kongah Babylon kah Judah hlangsol boeih loh rhunkhuennah la lo uh saeh. “Babylon manghai loh amih rhoi Zedekiah neh Ahab te hmai neh a rhoh bangla BOEIPA loh nang n'khueh,” ti saeh.
23 Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
Israel taengah boethaehalang a saii uh tih a hui kah yuu nen khaw samphaih uh. Amih ka uen pawt mai ah kai ming neh a honghi ol a thui uh. Kai laipai long he ka ming khaw ka ming ta. He tah BOEIPA kah olphong ni.
24 Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
Nehelam Shemaiah te khaw thui pah.
25 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
He ni Israel Pathen, caempuei BOEIPA loh a thui. Namah loh na ming neh Jerusalem kah pilnam boeih taengah, Maaseiah capa khosoih Zephaniah taeng neh khosoih boeih taengah ca pat lamtah thui pah,” ti nah.
26 ‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
BOEIPA loh khosoih Jehoiada yueng BOEIPA im kah hlangtawt la om ham khosoih la nang n'khueh coeng. Pavai neh tonghma hlang boeih te hloong khui neh thi rhawnmoep dongla khueh nawn.
27 To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
Te dongah balae tih nangmih taengah aka tonghma Anatoth Jeremiah te na tluung laeh pawh?
28 Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
He dongah nim Babylon kah mamih ham ol han tah. Im te puet thoh uh lamtah khosa uh, dum tue uh lamtah a thaih te ca uh a ti rhailai,'ti nah,” a ti.
29 Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
Tedae tekah cabu te khosoih Zephaniah loh tonghma Jeremiah kah a hna ah a tae pah.
30 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Te vaengah BOEIPA ol te Jeremiah taengla ha pawk.
31 “Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
vangsawn boeih taengah thui hamla tueih laeh. Nehelam Shemaiah kawng ni BOEIPA loh a thui coeng he. Shemaiah te nangmih taengah tonghma ngawn cakhaw kai loh anih kan tueih pawt dongah nangmih te a honghi dongah ni m'pangtung sak.
32 ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”
Te dongah BOEIPA loh he ni a. thui. Nehelam Shemaiah neh a tiingan te ka cawh coeng. Anih te he pilnam lakli ah hlang hing la om pawt vetih ka pilnam taengah a then ka saii te khaw hmu mahpawh. He tah BOEIPA kah olphong ni. Anih loh BOEIPA taengah koeknah ni a. thui.

< Irmiya 29 >