< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
Aynı yıl Yahuda Kralı Sidkiya'nın krallığının başlangıcında, dördüncü yılının beşinci ayında Givonlu Azzur oğlu Peygamber Hananya RAB'bin Tapınağı'nda kâhinlerle bütün halkın önünde bana şöyle dedi:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
“İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB diyor ki, ‘Babil Kralı'nın boyunduruğunu kıracağım.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Babil Kralı Nebukadnessar'ın buradan alıp Babil'e götürdüğü RAB'bin Tapınağı'na ait bütün eşyaları iki yıl içinde buraya geri getireceğim.
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
Yahuda Kralı Yehoyakim oğlu Yehoyakin'le Babil'e sürgüne giden bütün Yahudalılar'ı buraya geri getireceğim’ diyor RAB, ‘Çünkü Babil Kralı'nın boyunduruğunu kıracağım.’”
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Bunun üzerine Peygamber Yeremya, kâhinlerin ve RAB'bin Tapınağı'ndaki halkın önünde Peygamber Hananya'yı yanıtladı.
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
Yeremya şöyle dedi: “Amin! RAB aynısını yapsın! RAB, tapınağına ait eşyalarla bütün sürgünleri Babil'den buraya geri getirerek ettiğin peygamberlik sözlerini gerçekleştirsin!
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Yalnız şimdi sana ve halka söyleyeceğim şu sözü dinle:
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Çok önce, benden de senden de önce yaşamış peygamberler birçok ülke ve büyük krallığın başına savaş, felaket, salgın hastalık gelecek diye peygamberlik ettiler.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
Ancak esenlik olacağını söyleyen peygamberin sözü yerine gelirse, onun gerçekten RAB'bin gönderdiği peygamber olduğu anlaşılır.”
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Bunun üzerine Peygamber Hananya, Peygamber Yeremya'nın boynundan boyunduruğu çıkarıp kırdı.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Sonra halkın önünde şöyle dedi: “RAB diyor ki, ‘Babil Kralı Nebukadnessar'ın bütün ulusların boynuna taktığı boyunduruğu iki yıl içinde işte böyle kıracağım.’” Böylece Peygamber Yeremya yoluna gitti.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Peygamber Hananya Peygamber Yeremya'nın boynundaki boyunduruğu kırdıktan sonra RAB Yeremya'ya şöyle seslendi:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
“Git, Hananya'ya de ki, ‘RAB şöyle diyor: Sen tahtadan yapılmış boyunduruğu kırdın, ama yerine demir boyunduruk yapacaksın!
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
Çünkü İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB diyor ki, Babil Kralı Nebukadnessar'a kulluk etmeleri için bütün bu ulusların boynuna demir boyunduruk geçirdim, ona kulluk edecekler. Yabanıl hayvanları da onun denetimine vereceğim.’”
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Peygamber Yeremya Peygamber Hananya'ya, “Dinle, ey Hananya!” dedi, “Seni RAB göndermedi. Ama sen bu ulusu yalana inandırdın.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
Bu nedenle RAB diyor ki, ‘Seni yeryüzünden silip atacağım. Bu yıl öleceksin. Çünkü halkı RAB'be karşı kışkırttın.’”
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Peygamber Hananya o yılın yedinci ayında öldü.

< Irmiya 28 >