< Irmiya 28 >
1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
Men samma år, i begynnelsen av Sidkias, Juda konungs, regering, i femte månaden av hans fjärde regeringsår, talade profeten Hananja, Assurs son, från Gibeon, så till mig i HERRENS hus, i prästernas och allt folkets närvaro; han sade:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
"Så säger HERREN Sebaot, Israels Gud: Jag skall sönderbryta den babyloniske konungens ok.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Inom två års tid skall jag föra tillbaka till denna plats alla de kärl i HERRENS hus, som Nebukadnessar, konungen i Babel, har tagit bort ifrån denna plats och fört till Babel.
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
Och Jekonja, Jojakims son, Juda konung, och alla fångar ifrån Juda, som hava kommit till Babel, skall jag föra tillbaka till denna plats, säger HERREN; ty jag skall sönderbryta den babyloniske konungens ok."
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Men profeten Jeremia svarade profeten Hananja, i närvaro av prästerna och allt det folk som stod i HERRENS hus;
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
profeten Jeremia sade: "Amen. Så göre HERREN. Det som du har profeterat må HERREN uppfylla, i det att han för tillbaka från Babel till denna plats de kärl som funnos i HERRENS hus, så ock alla fångarna.
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Men hör dock detta ord som jag vill tala inför dig och allt folket.
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Forna tiders profeter, de som hava varit före mig och dig, hava mot mäktiga länder och stora riken profeterat om krig, olycka och pest.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
Därför, om nu en profet profeterar om lycka, så kan man först då när den profetens ord går i fullbordan veta att han är en profet som HERREN i sanning har sänt."
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Då tog profeten Hananja oket från profeten Jeremias hals och bröt sönder det.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Och Hananja sade i allt folkets närvaro: "Så säger HERREN: Just så skall jag inom två års tid bryta sönder den babyloniske konungen Nebukadnessars ok och taga det från alla folkens hals." Men profeten Jeremia gick sin väg.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Sedan, efter det att profeten Hananja hade brutit sönder oket och tagit det från profeten Jeremias hals, kom HERRENS ord till Jeremia; han sade:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
"Gå åstad och säg till Hananja: Så säger HERREN: Ett ok av trä har du brutit sönder, men i dess ställe har du skaffat ett ok av järn.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
Ty så säger HERREN Sebaot, Israels Gud: Ett ok av järn skall jag sätta på alla dessa folks hals, för att de må tjäna Nebukadnessar, konungen i Babel; ty honom skola de tjäna. Ja ock markens djur har jag givit honom."
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Och profeten Jeremia sade ytterligare till profeten Hananja: "Hör, du Hananja: HERREN har icke sänt dig; du har förlett detta folk att sätta sin lit till lögn.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
Därför säger HERREN så: Se, jag skall taga dig bort ifrån jorden. I detta år skall du dö, eftersom du har predikat avfall från HERREN."
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Och samma år, i sjunde månaden, dog profeten Hananja.