< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
در همان سال، در ابتدای سلطنت صدقیا، پادشاه یهودا، در ماه پنجم از سال چهارم، یک نبی دروغین به نام حننیا (پسر عزور)، اهل جبعون، در خانهٔ خداوند ایستاد و در مقابل کاهنان و مردم، رو به من کرد و گفت:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
«خداوند لشکرهای آسمان، خدای اسرائیل می‌فرماید: من یوغ بندگی پادشاه بابِل را از گردن شما برمی‌دارم.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
بعد از دو سال، تمام ظروف و اشیاء گرانبهای خانۀ خداوند را که نِبوکَدنِصَّر به بابِل برده، پس خواهم آورد.
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
یهویاکین (پسر یهویاقیم) پادشاه یهودا را نیز با تمام کسانی که به بابِل به اسارت رفته‌اند، به اینجا باز خواهم گرداند. بله، من یوغی را که پادشاه بابِل بر گردن شما گذاشته، خواهم شکست. من، خداوند، این را می‌گویم.»
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
آنگاه من در حضور کاهنان و مردمی که در خانهٔ خدا جمع شده بودند، به حننیا گفتم:
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
«آمین! خدا کند پیشگویی‌های تو همه عملی شوند! امیدوارم هر چه گفتی، خداوند همان را بکند و گنجینه‌های این عبادتگاه را با تمام عزیزان ما که در بابِل اسیرند، باز آورد.
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
ولی حال در حضور تمام این مردم به سخنان من گوش بده!
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
انبیای گذشته که پیش از من و تو بوده‌اند، اکثراً بر ضد قومهای دیگر پیشگویی می‌کردند و همیشه از جنگ و قحطی، بلا و مرض خبر می‌دادند.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
اما آن نبی‌ای که دربارهٔ صلح و آرامش پیشگویی می‌کند، زمانی ثابت می‌شود که از جانب خداوند سخن گفته است که پیشگویی‌اش به انجام برسد.»
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
آنگاه حننیای نبی یوغی را که بر گردن من بود، برداشت و آن را شکست.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
سپس به جمعیتی که در آنجا بودند، گفت: «خداوند قول داده است که دو سال دیگر یوغ نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل را به همین شکل از گردن قومها بردارد و آن را بشکند و ایشان را آزاد سازد.» با شنیدن سخنان او، من از آنجا بیرون رفتم.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
پس از مدتی خداوند به من فرمود:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
«برو به حننیا بگو که خداوند چنین می‌فرماید:”تو یوغ چوبین را شکستی، ولی یوغ آهنین جای آن را خواهد گرفت.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
خداوند لشکرهای آسمان، خدای اسرائیل می‌فرماید: من بر گردن تمام این قومها، یوغ آهنین گذاشته‌ام تا نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل را بندگی نمایند. حتی تمام حیوانات وحشی را مطیع او ساخته‌ام!“»
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
آنگاه به حننیا گفتم: «حننیا، گوش کن! خداوند تو را نفرستاده و با تو سخن نگفته است. تو می‌خواهی مردم را مجبور کنی که به وعده‌های دروغین تو امید ببندند.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
از این جهت خداوند فرموده که تو خواهی مرد؛ همین امسال عمرت به پایان خواهد رسید، چون مردم را علیه خداوند شورانیده‌ای!»
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
دو ماه بعد، حننیا مرد.

< Irmiya 28 >