< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
Un tanī gadā, Cedeķijas, Jūda ķēniņa, valdīšanas iesākumā, ceturtā gadā, piektā mēnesī, pravietis Kananija, Acura dēls, no Gibeonas, runāja uz mani Tā Kunga namā priekš priesteru un visu ļaužu acīm un sacīja:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
Tā runā Tas Kungs Cebaot, Israēla Dievs, un saka: Es Bābeles ķēniņa jūgu esmu salauzis.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Vēl būs divi pilni gadi, tad Es atkal uz šo vietu atvedīšu visus Tā Kunga nama rīkus, ko Nebukadnecars, Bābeles ķēniņš, ir paņēmis no šīs vietas un aizvedis uz Bābeli.
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
Un Jekaniju, Jojaķima dēlu, Jūda ķēniņu, un visus no Jūda aizvestos, kas uz Bābeli nākuši, Es atvedīšu uz šo vietu, saka Tas Kungs, jo Es salauzīšu Bābeles ķēniņa jūgu.
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Tad pravietis Jeremija sacīja uz pravieti Kananiju priekš priesteru un visu ļaužu acīm, kas tur stāvēja Tā Kunga namā,
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
Un pravietis Jeremija sacīja: Āmen! Tā lai Tas Kungs dara, lai Tas Kungs tavus vārdus apstiprina, ko tu esi sludinājis, ka Viņš atved Dieva nama rīkus un visus aizvestos no Bābeles atkal uz šo vietu.
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Bet klausi jel šo vārdu, ko es runāšu priekš tavām ausīm un priekš visu ļaužu ausīm.
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Tie pravieši, kas no sen laikiem priekš manis un priekš tevis bijuši, tie pret daudz zemēm un lielām valstīm sludinājuši par karu un par postu un par mēri.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
Bet tas pravietis, kas mieru sludina, kad tā pravieša vārds notiek, tiks atzīts par pravieti, ko Tas Kungs tiešām sūtījis.
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Tad pravietis Kananija ņēma to jūgu no pravieša Jeremijas kakla un to salauza.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Un Kananija runāja priekš visu ļaužu acīm un sacīja: tā saka Tas Kungs: tāpat Es salauzīšu Nebukadnecara, Bābeles ķēniņa, jūgu, no visu ļaužu kakla, pirms divi gadi būs pagalam. Un pravietis Jeremija gāja savu ceļu.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Tad Tā Kunga vārds notika uz Jeremiju, kad pravietis Kananija to jūgu no pravieša Jeremijas kakla bija salauzis, un sacīja:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
Ej un runā uz Kananiju un saki: tā saka Tas Kungs: koka jūgus tu esi salauzis, bet viņu vietā taisījis dzelzs jūgus.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
Jo tā saka Tas Kungs Cebaot, Israēla Dievs: dzelzs jūgu Es visiem šiem ļaudīm esmu licis ap kaklu, ka tiem būs kalpot Nebukadnecaram, Bābeles ķēniņam, un tiem būs viņam kalpot, jo pat zvērus laukā Es viņam esmu devis.
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Un pravietis Jeremija sacīja uz pravieti Kananiju: klausi jel, Kananija! Tas Kungs tevi nav sūtījis, un tu dari, ka šie ļaudis paļaujas uz meliem.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
Tādēļ Tas Kungs tā saka: redzi! Es tevi atmetīšu no zemes virsas; šinī gadā tu mirsi, jo tu esi mācījis atkāpties no Tā Kunga.
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Tā pravietis Kananija nomira tanī gadā, septītā mēnesī.

< Irmiya 28 >