< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
Et il arriva en cette année-là, au commencement du règne de Sédécias, roi de Juda, en la quatrième année, au cinquième mois, qu’Hananias, fils d’Azur, prophète de Gabaon, me parla dans la maison du Seigneur, devant les prêtres et tout le peuple, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
Voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël; J’ai brisé le joug du roi de Babylone.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Encore deux ans de jours, et moi je ferai rapporter ici tous les vases de la maison du Seigneur, que Nabuchodonosor, roi de Babylone, a enlevés de ce lieu-ci, et qu’il a transportés à Babylone,
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
Et je ferai revenir, dit le Seigneur, Jéchonias, fils de Joakim, roi de Juda, et tous les fils de la transmigration de Juda qui sont entrés à Babylone, car je briserai le joug du roi de Babylone.
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Et Jérémie le prophète dit à Hananias le prophète, sous les yeux des prêtres et sous les yeux de tout le peuple qui se tenait dans la maison du Seigneur;
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
Jérémie, le prophète, dit donc: Amen, qu’ainsi fasse le Seigneur; que le Seigneur réalise tes paroles que tu as prophétisées, afin que les vases soient rapportés dans la maison du Seigneur, et que tous les fils de la transmigration de Babylone reviennent en ce lieu.
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Mais cependant écoute cette parole que moi, je dis à tes oreilles et aux oreilles de tout le peuple:
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Les prophètes qui ont été avant moi et avant toi dès le commencement, ont prophétisé dans beaucoup de pays et dans de grands royaumes, la guerre, et l’affliction, et la famine.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
Le prophète qui prédit la paix, lorsque sa parole s’accomplira, sera reconnu pour le prophète que le Seigneur a envoyé véritablement.
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Et Hananias le prophète enleva la chaîne du cou de Jérémie, le prophète, et la brisa.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Et Hananias parla en présence de tout le peuple, disant: Voici ce que di t le Seigneur: Ainsi je briserai après deux années de jours le joug de Nabuchodonosor, roi de Babylone, et je l’ôterai du cou de toutes les nations.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et Jérémie, le prophète, reprit son chemin. Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, après qu’Hananias, le prophète, eut brisé la chaîne, l’ayant ôtée du cou de Jérémie, le prophète, disant:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
Va, et tu diras à Hananias: Voici ce que dit le Seigneur: Tu as brisé des chaînes de bois, et tu feras en leur place des chaînes de fer.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
Car voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: J’ai posé un joug de fer sur le cou de toutes les nations, afin qu’elles se soumettent à Nabuchodonosor, roi de Babylone, et elles se soumettront à lui; de plus je lui ai même donné les bêtes de la terre.
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Et Jérémie le prophète dit à Hananias le prophète: Ecoute, Hananias; le Seigneur ne t’a pas envoyé, et tu as fait que ce peuple s’est confié dans un mensonge.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
C’est pourquoi, voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je te chasserai de la face de la terre; cette année tu mourras; car tu as parlé contre le Seigneur.
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Et Hananias mourut cette année-là, au septième mois.

< Irmiya 28 >