< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
II arriva, en cette même année, au début du règne de Sédécias, roi de Juda, le cinquième mois de la quatrième année, que Hanania, fils d’Azzour, prophète natif de Gabaon, me tint ce discours dans le Temple de l’Eternel, en présence des prêtres et de tout le peuple:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
"Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: Je brise le joug du roi de Babylone.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Encore deux années, et je ferai réintégrer dans cette cité tous les vases du Temple de l’Eternel, que Nabuchodonosor, roi de Babylone, a enlevés d’ici et transportés à Babylone.
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
Et leconia aussi, fils de Joïakim, roi de Juda, avec tous les déportés de Juda, qui sont arrivés à Babylone, je les ramènerai en ces lieux, dit l’Eternel, car je vais briser le joug du roi de Babylone."
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Alors le prophète Jérémie répliqua au prophète Hanania en présence des prêtres et en présence de tout le peuple qui se tenait dans la maison de l’Eternel,
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
et le prophète Jérémie dit: "Amen! Ainsi fasse l’Eternel! Puisse l’Eternel accomplir la prédiction que tu as énoncée, en faisant revenir de Babylone en cette cité les vases du Temple de l’Eternel!
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Toutefois écoute, je t’en prie, la parole que je fais entendre à tes oreilles et aux oreilles de tout le peuple.
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Les prophètes qui nous ont précédés, moi et toi, de toute antiquité, ont prédit à de puissants pays et à de grands rois des guerres, des calamités et des pestes.
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
Mais le prophète qui prédit un événement heureux n’est reconnu comme véritablement envoyé de Dieu qu’autant que sa prédiction s’accomplit."
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Alors le prophète Hanania saisit le joug posé sur le cou du prophète Jérémie et le brisa.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Et Hanania prononça ces paroles en présence de tout le peuple: "Ainsi parle l’Eternel: C’Est de cette façon que, dans un délai de deux ans, je briserai le joug que Nabuchodonosor, roi de Babylone, fait peser sur le cou de tous les peuples." Le prophète Jérémie se retira, poursuivant son chemin.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Puis la parole de l’Eternel fut adressée à Jérémie en ces termes, après que le prophète Hanania eût brisé le joug posé sur le cou de Jérémie:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
"Va et tiens à Hanania ce langage: Tu as brisé un joug de bois, tu le remplaceras par un joug de fer;
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
car voici ce que dit l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: C’Est un joug de fer que je pose sur le cou de tous ces peuples, pour qu’ils soient soumis à Nabuchodonosor, roi de Babylone, et le servent; jusqu’aux animaux des champs, je les lui livre."
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Puis le prophète Jérémie dit au prophète Hanania: "Veuille écouter, Hanania! l’Eternel ne t’a pas envoyé et toi, tu as leurré ce peuple par des promesses mensongères.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
C’Est pourquoi l’Eternel parle ainsi: Je vais te renvoyer de la surface de la terre; au cours de cette année tu mourras, parce que tu as prêché la révolte contre l’Eternel."
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
En effet, le prophète Hanania mourut cette même année, dans le septième mois.

< Irmiya 28 >