< Irmiya 28 >

1 A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
Et il arriva, en cette même année, au commencement du règne de Sédécias, roi de Juda, en la quatrième année, au cinquième mois, que Hanania, fils d’Azzur, le prophète, qui était de Gabaon, me parla dans la maison de l’Éternel, aux yeux des sacrificateurs et de tout le peuple, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
Ainsi a parlé l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël, disant: J’ai brisé le joug du roi de Babylone.
3 Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
Encore deux années, et je ferai revenir en ce lieu tous les ustensiles de la maison de l’Éternel que Nebucadnetsar, roi de Babylone, a pris de ce lieu et a transportés à Babylone;
4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
et Jéconias, fils de Jehoïakim, roi de Juda, et tous les transportés de Juda qui sont allés à Babylone, je les ramènerai dans ce lieu, dit l’Éternel; car je briserai le joug du roi de Babylone.
5 Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
Et Jérémie le prophète parla à Hanania, le prophète, aux yeux des sacrificateurs et aux yeux de tout le peuple, qui se tenaient dans la maison de l’Éternel.
6 Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
Et Jérémie le prophète dit: Amen! Qu’ainsi fasse l’Éternel! Que l’Éternel confirme tes paroles, que tu as prophétisées, pour faire revenir de Babylone en ce lieu les ustensiles de la maison de l’Éternel et tous les captifs!
7 Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
Toutefois, écoute, je te prie, cette parole que je prononce à tes oreilles et aux oreilles de tout le peuple:
8 Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
Les prophètes qui ont été avant moi et avant toi, d’ancienneté, ont aussi prophétisé, touchant plusieurs pays et touchant de grands royaumes, la guerre, et le malheur, et la peste;
9 Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
le prophète qui prophétise la paix, quand la parole de ce prophète arrivera, on saura que c’est un prophète que l’Éternel a véritablement envoyé.
10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
Et Hanania le prophète prit le joug de dessus le cou de Jérémie le prophète, et le brisa.
11 ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
Et Hanania parla aux yeux de tout le peuple, disant: Ainsi dit l’Éternel: Encore deux années, et je briserai ainsi le joug de Nebucadnetsar, roi de Babylone, de dessus le cou de toutes les nations. Et Jérémie le prophète s’en alla son chemin.
12 Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à Jérémie, après que Hanania le prophète eut brisé le joug de dessus le cou de Jérémie le prophète, disant:
13 “Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
Va, et parle à Hanania, disant: Ainsi dit l’Éternel: Tu as brisé les jougs de bois, et tu as fait à leur place des jougs de fer.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
Car ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: J’ai mis un joug de fer sur le cou de toutes ces nations, afin qu’elles servent Nebucadnetsar, roi de Babylone; et elles le serviront; et je lui ai aussi donné les bêtes des champs.
15 Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
Et Jérémie le prophète dit à Hanania le prophète: Écoute, Hanania! L’Éternel ne t’a point envoyé; mais tu as fait que ce peuple s’est confié au mensonge.
16 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel: Voici, je te renvoie de dessus la face de la terre; tu mourras cette année, car tu as parlé de révolte contre l’Éternel.
17 A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Et Hanania le prophète mourut cette année-là, au septième mois.

< Irmiya 28 >