< Irmiya 27 >

1 A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
Yahuda Kralı Yoşiya oğlu Sidkiya'nın krallığının başlangıcında RAB Yeremya'ya seslendi:
2 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
RAB bana dedi ki, “Kendine sırımla bağlanmış tahta bir boyunduruk yap, boynuna geçir.
3 Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
Sonra Yeruşalim'e, Yahuda Kralı Sidkiya'ya gelen ulaklar aracılığıyla Edom, Moav, Ammon, Sur ve Sayda krallarına haber gönder.
4 Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
Efendilerine şunu bildirmelerini buyur: İsrail'in Tanrısı Her Şeye Egemen RAB diyor ki, ‘Efendilerinize söyleyin:
5 Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
Yeryüzünü de üstünde yaşayan insanlarla hayvanları da büyük gücümle, kudretli elimle ben yarattım. Onu uygun gördüğüm kişiye veririm.
6 Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
Şimdi bütün bu ülkeleri Babil Kralı kulum Nebukadnessar'a vereceğim. Yabanıl hayvanları da kulluk etsinler diye ona vereceğim.
7 Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
Ülkesi için saptanan zaman gelinceye dek bütün uluslar ona, oğluna, torununa kulluk edecek. Sonra birçok ulus, büyük krallar onu köle edecekler.
8 “‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
“‘Hangi ulus ya da krallık Babil Kralı Nebukadnessar'a kulluk edip boyunduruğuna girmezse, o ulusu onun eline teslim edene dek kılıçla, kıtlıkla, salgın hastalıkla cezalandıracağım, diyor RAB.
9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
Size gelince, peygamberlerinizi, falcılarınızı, düş görenlerinizi, medyumlarınızı, büyücülerinizi dinlemeyin! Onlar size, Babil Kralı'na kulluk etmeyeceksiniz diyorlar.
10 Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
Size yalan peygamberlik ediyorlar. Bunun sonucu sizi ülkenizden uzaklaştırmak oluyor. Sizi süreceğim, yok olacaksınız.
11 Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
Ama Babil Kralı'nın boyunduruğuna girip ona kulluk eden ulusu kendi toprağında bırakacağım, diyor RAB. O ulus toprağını işleyecek, orada yaşayacak.’”
12 Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
Yahuda Kralı Sidkiya'ya bütün bu sözleri ilettim. Dedim ki, “Boyunlarınızı Babil Kralı'nın boyunduruğu altına koyun. Ona ve halkına kulluk edin ki sağ kalasınız.
13 Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
RAB'bin Babil Kralı'na kulluk etmeyen her ulus için dediği gibi, niçin sen ve halkın kılıç, kıtlık, salgın hastalık yüzünden ölesiniz?
14 Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
Size, ‘Babil Kralı'na kulluk etmeyeceksiniz’ diyen peygamberlerin sözlerine kulak asmayın. Onlar size yalan peygamberlik ediyorlar.
15 ‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
‘Onları ben göndermedim’ diyor RAB, ‘Adımla yalan peygamberlik ediyorlar. Bu yüzden sizi de size peygamberlik eden peygamberleri de süreceğim, hepiniz yok olacaksınız.’”
16 Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
Sonra kâhinlerle halka şöyle dedim: “RAB diyor ki, ‘İşte RAB'bin Tapınağı'nın eşyaları yakında Babil'den geri getirilecek’ diyen peygamberlerinize kulak asmayın. Onlar size yalan peygamberlik ediyorlar.
17 Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
Onları dinlemeyin. Sağ kalmak için Babil Kralı'na kulluk edin. Bu kent neden viraneye çevrilsin?
18 In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
Eğer bunlar peygamberse ve RAB'bin sözü onlardaysa, RAB'bin Tapınağı'nda, Yahuda Kralı'nın sarayında ve Yeruşalim'de kalan eşyalar Babil'e götürülmesin diye Her Şeye Egemen RAB'be yalvarsınlar.
19 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
“Çünkü Babil Kralı Nebukadnessar Yahuda Kralı Yehoyakim oğlu Yehoyakin'i Yahuda ve Yeruşalim soylularıyla birlikte Yeruşalim'den Babil'e sürdüğünde alıp götürmediği sütunlar, havuz, ayaklıklar ve kentte kalan öbür eşyalar için Her Şeye Egemen RAB şöyle diyor.
20 waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
21 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
Evet, RAB'bin Tapınağı'nda, Yahuda Kralı'nın sarayında ve Yeruşalim'de kalan eşyalar için İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB şöyle diyor:
22 ‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”
‘Bunlar Babil'e alınıp götürülecek, aldıracağım güne dek de orada kalacaklar’ diyor RAB, ‘O zaman onları alacak, yeniden buraya yerleştireceğim.’”

< Irmiya 27 >