< Irmiya 27 >

1 A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
Au commencement du règne de Jéhojakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole fut adressée par l'Éternel à Jérémie, en ces termes:
2 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
L'Éternel me dit ainsi: Fais-toi des liens et des jougs, et mets-les sur ton cou;
3 Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
Et envoie-les au roi d'Édom, au roi de Moab, au roi des enfants d'Ammon, au roi de Tyr, et au roi de Sidon, par les mains des ambassadeurs qui viennent à Jérusalem, vers Sédécias, roi de Juda.
4 Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
Et donne-leur mes ordres pour leurs maîtres, en disant: Ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Vous direz ainsi à vos maîtres:
5 Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
J'ai fait la terre, les hommes et les bêtes qui sont sur la terre, par ma grande force et par mon bras étendu; et je les donne à qui bon me semble.
6 Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
Et maintenant, j'ai livré tous ces pays entre les mains de Nébucadnetsar, roi de Babylone, mon serviteur; et même je lui ai donné les bêtes des champs, pour qu'elles lui soient assujetties.
7 Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
Et toutes les nations lui seront assujetties, à lui et à son fils, et au fils de son fils, jusqu'à ce que le temps de son pays lui-même vienne aussi, et que plusieurs nations et de grands rois l'asservissent.
8 “‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
Et il arrivera que la nation ou le royaume qui ne se soumettra pas à lui, à Nébucadnetsar, roi de Babylone, et qui ne soumettra pas son cou au joug du roi de Babylone, je punirai cette nation-là, dit l'Éternel, par l'épée, par la famine et par la peste, jusqu'à ce que je les aie consumés par sa main.
9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
Vous donc, n'écoutez pas vos prophètes, ni vos devins, ni vos songeurs, ni vos augures, ni vos magiciens qui vous parlent, disant: Vous ne serez point assujettis au roi de Babylone.
10 Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
Car ils vous prophétisent le mensonge, pour que vous alliez loin de votre pays, afin que je vous en chasse et que vous périssiez.
11 Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
Mais la nation qui soumettra son cou au joug du roi de Babylone et le servira, je la laisserai dans son pays, dit l'Éternel, afin qu'elle le cultive et y demeure.
12 Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
Puis je parlai à Sédécias, roi de Juda, conformément à toutes ces paroles, en disant: Soumettez-vous au joug du roi de Babylone, et servez-le, lui et son peuple, et vous vivrez.
13 Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
Pourquoi mourriez-vous, toi et ton peuple, par l'épée, par la famine et par la peste, selon que l'Éternel l'a dit de la nation qui ne se soumettrait pas au roi de Babylone?
14 Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
N'écoutez donc pas les paroles des prophètes qui vous parlent en disant: Vous ne serez point assujettis au roi de Babylone! Car ils vous prophétisent le mensonge.
15 ‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
Je ne les ai pas envoyés, dit l'Éternel, et ils prophétisent faussement en mon nom, afin que je vous chasse et que vous périssiez, vous et les prophètes qui vous prophétisent.
16 Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
Je parlai aussi aux sacrificateurs et à tout ce peuple, et je leur dis: Ainsi a dit l'Éternel: N'écoutez pas les paroles de vos prophètes, qui vous prophétisent, en disant: Voici, les vases de la maison de l'Éternel seront bientôt rapportés de Babylone! Car ils vous prophétisent le mensonge.
17 Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
Ne les écoutez pas. Soumettez-vous au roi de Babylone et vous vivrez. Pourquoi cette ville deviendrait-elle une ruine?
18 In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
Et s'ils sont prophètes et si la parole de l'Éternel est avec eux, qu'ils intercèdent donc auprès de l'Éternel des armées pour que les ustensiles restant dans la maison de l'Éternel et dans la maison du roi de Juda et à Jérusalem, n'aillent point à Babylone.
19 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
Car ainsi a dit l'Éternel des armées, touchant les colonnes, et la mer, et les socles, et les autres ustensiles qui sont restés dans cette ville,
20 waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
Que Nébucadnetsar, roi de Babylone, n'a pas emportés quand il a transporté de Jérusalem à Babylone Jéchonias, fils de Jéhojakim, roi de Juda, avec tous les grands de Juda et de Jérusalem;
21 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
Ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël, au sujet des ustensiles qui restent dans la maison de l'Éternel, et dans la maison du roi de Juda, et à Jérusalem:
22 ‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”
Ils seront emportés à Babylone, et ils y resteront jusqu'au jour où je les chercherai, dit l'Éternel, où je les ferai remonter, et revenir en ce lieu.

< Irmiya 27 >