< Irmiya 27 >

1 A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
Au commencement du règne de Jehoïakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole vint de par l’Éternel à Jérémie, disant:
2 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
Ainsi me dit l’Éternel: Fais-toi des liens et des jougs, et mets-les sur ton cou;
3 Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
et envoie-les au roi d’Édom, et au roi de Moab, et au roi des fils d’Ammon, et au roi de Tyr, et au roi de Sidon, par la main des messagers qui sont venus à Jérusalem vers Sédécias, roi de Juda;
4 Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
et commande-leur, pour leurs seigneurs, disant: Ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Vous direz ainsi à vos seigneurs:
5 Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
Moi, j’ai fait la terre, l’homme et la bête qui sont sur la face de la terre, par ma grande puissance et par mon bras étendu, et je les ai donnés à qui il était bon à mes yeux.
6 Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
Et maintenant j’ai livré tous ces pays en la main de Nebucadnetsar, roi de Babylone, mon serviteur, et je lui ai aussi donné les bêtes des champs pour le servir.
7 Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
Et toutes les nations le serviront, lui, et son fils et le fils de son fils, jusqu’à ce que vienne le temps de son pays aussi, et que plusieurs nations et de grands rois l’asservissent.
8 “‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
Et il arrivera que la nation ou le royaume qui ne le servira pas, lui, Nebucadnetsar, roi de Babylone, et qui n’aura pas mis son cou sous le joug du roi de Babylone, je visiterai cette nation, dit l’Éternel, par l’épée, et par la famine, et par la peste, jusqu’à ce que je les aie consumés par sa main.
9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
Et vous, n’écoutez pas vos prophètes, et vos devins, et vos songeurs, et vos pronostiqueurs, et vos magiciens, qui vous parlent, disant: Vous ne servirez point le roi de Babylone.
10 Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
Car ils vous prophétisent le mensonge, pour vous faire aller loin de votre terre, et pour que je vous jette dehors, et que vous périssiez.
11 Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
Et la nation qui mettra son cou sous le joug du roi de Babylone et le servira, je la laisserai dans sa terre, dit l’Éternel, et elle la labourera et y demeurera.
12 Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
Et je parlai à Sédécias, roi de Juda, selon toutes ces paroles, disant: Prêtez vos cous au joug du roi de Babylone, et servez-le, lui et son peuple, et vous vivrez.
13 Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
Pourquoi mourriez-vous, toi et ton peuple, par l’épée, par la famine, et par la peste, selon que l’Éternel a parlé contre la nation qui ne servira pas le roi de Babylone?
14 Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
Et n’écoutez pas les paroles des prophètes qui vous parlent, disant: Vous ne servirez pas le roi de Babylone; car ils vous prophétisent le mensonge.
15 ‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
Car je ne les ai pas envoyés, dit l’Éternel, et ils prophétisent le mensonge en mon nom, afin que je vous jette dehors et que vous périssiez, vous et les prophètes qui vous prophétisent.
16 Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
Et je parlai aux sacrificateurs et à tout ce peuple, disant: Ainsi dit l’Éternel: N’écoutez point les paroles de vos prophètes qui vous prophétisent, disant: Voici, les ustensiles de la maison de l’Éternel vont bientôt revenir de Babylone; car c’est le mensonge qu’ils vous prophétisent.
17 Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
Ne les écoutez pas; servez le roi de Babylone, et vivez. Pourquoi cette ville serait-elle un désert?
18 In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
Et s’ils sont prophètes, et si la parole de l’Éternel est avec eux, qu’ils intercèdent auprès de l’Éternel des armées, afin que les ustensiles qui restent dans la maison de l’Éternel, et dans la maison du roi de Juda, et à Jérusalem, n’aillent point à Babylone.
19 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
Car ainsi dit l’Éternel des armées touchant les colonnes, et touchant la mer, et touchant les socles, et touchant le reste des ustensiles qui sont de reste dans cette ville,
20 waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
que n’a pas pris Nebucadnetsar, roi de Babylone, quand il transporta de Jérusalem à Babylone Jéconias, fils de Jehoïakim, roi de Juda, et tous les nobles de Juda et de Jérusalem; –
21 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
car ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël, touchant les ustensiles qui restent dans la maison de l’Éternel, et dans la maison du roi de Juda, et à Jérusalem:
22 ‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”
Ils seront emportés à Babylone, et ils seront là jusqu’au jour où je m’en occuperai, dit l’Éternel, et où je les ferai remonter et revenir dans ce lieu.

< Irmiya 27 >