< Irmiya 27 >

1 A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
U početku kraljevanja Sidkije, sina Jošije, kralja judejskoga, uputi Jahve Jeremiji ovu riječ.
2 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
Ovako mi reče Jahve: “Načini sebi užad i jaram i stavi ga sebi na vrat.
3 Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
Zatim poruči kralju edomskom, kralju moapskom, kralju amonskom, kralju tirskom i kralju sidonskom, po njihovim izaslanicima koji su došli u Jeruzalem kralju judejskom Sidkiji.
4 Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
Naredi im da poruče svojim gospodarima: 'Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov! Ovako poručite svojim gospodarima:
5 Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
Ja sam snagom svojom svesilnom i rukom ispruženom stvorio zemlju, ljude i životinje na zemlji. I ja to dajem kome hoću.
6 Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
Sada, dakle, sve te zemlje dajem u ruke Nabukodonozoru, kralju babilonskom, sluzi svojemu; dajem mu i poljsko zvijerje da mu služi.
7 Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
I svi će narodi služiti njemu i njegovu sinu, i sinu njegova sina, dok i njegovoj zemlji ne kucne čas te i njega ne upokore moćni narodi i veliki kraljevi.
8 “‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
Ako koji narod, ili kraljevstvo, ne htjedne služiti Nabukodonozora, kralja babilonskoga, ne hoteć' se upregnuti u jaram kralja babilonskog, taj ću narod kazniti mačem, glađu i kugom - riječ je Jahvina - dok ga sasvim ne zatrem rukom njegovom.
9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
Ne slušajte, dakle, svojih proroka, gatalaca, sanjara, zvjezdara svojih i čarobnjaka koji vam govore: 'Ne, vi nećete služiti kralju babilonskom!'
10 Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
Jer vam oni laž prorokuju samo da vas udalje iz vaše zemlje, da vas otjeram pa da propadnete.
11 Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
Ali narod koji se upregne u jaram kralja babilonskoga da mu služi ostavit ću na miru u zemlji njegovoj - riječ je Jahvina - da je obrađuje i u njoj živi.'”
12 Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
Sve sam to rekao Sidkiji, kralju judejskom, govoreći: “Upregnite se u jaram kralja babilonskoga i pokorite se njemu i narodu njegovu da ostanete živi.
13 Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
Zašto da poginete, ti i narod tvoj, od mača, gladi i kuge, kao što se Jahve zaprijetio narodu koji se ne podvrgne kralju babilonskom?
14 Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
Ne slušajte, dakle, riječi onih proroka koji vam govore: 'Vi nećete služiti kralju babilonskom.' Oni vam laž prorokuju.
15 ‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
'Jer nisam ih ja poslao da vam prorokuju - riječ je Jahvina - nego vam oni laž prorokuju u moje ime, da vas otjeram iz vaše zemlje, pa da propadnete - vi i proroci koji vam prorokuju.'”
16 Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
I svećenicima i svemu ovom narodu rekao sam: “Ovako govori Jahve: 'Ne slušajte riječi svojih proroka koji vam ovako prorokuju: Evo, posuđe Doma Jahvina bit će uskoro vraćeno iz Babilona.' Oni vam laži prorokuju.
17 Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
Ne slušajte ih! Pokorite se kralju babilonskom da ostanete živi! Zašto da ovaj grad postane ruševina?
18 In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
Ako su oni zaista proroci, te ako je u njima riječ Jahvina, neka mole Jahvu nad Vojskama da i posuđe što još ostade u Domu Jahvinu i u dvoru kraljeva judejskih i u Jeruzalemu ne dospije u Babilon!
19 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
Jer ovako govori Jahve o stupovima, moru, podnožjima i o preostalom posuđu što još ostade u ovome gradu -
20 waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
što još Nabukodonozor, kralj babilonski, ne uze sa sobom onda kad odvede u izgnanstvo iz Jeruzalema u Babilon Jekoniju, sina Jojakimova, kralja judejskoga, i sve odličnike judejske i jeruzalemske.
21 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
Da, ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov, o posuđu koje preostade u Domu Jahvinu, u dvoru kralja judejskog, i u Jeruzalemu:
22 ‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”
'U Babilon će ih odnijeti i ondje će ostati sve do dana kad ja odem po njih - riječ je Jahvina. I ja ću sve to donijeti i postaviti na ovo mjesto!'”

< Irmiya 27 >