< Irmiya 26 >
1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Au commencement du règne de Joakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
Voici ce que dit le Seigneur: Tiens-toi dans le parvis de la maison du Seigneur, et tu diras à toutes les cités de Juda d’où l’on vient afin d’adorer dans la maison du Seigneur, tous les discours que moi je t’ai commandé de leur adresser; ne retranche pas une parole,
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Pour voir si par hasard ils écouteront, et s’ils se convertiront, chacun de sa voie mauvaise, et je me repentirai du mal que je pense leur faire, à cause de la malice de leurs œuvres.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur: Si vous ne m’écoutez pas, quand j’ordonne que vous marchiez dans ma loi que je vous ai donnée,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
Et que vous entendiez les paroles de mes serviteurs les prophètes, que moi j’ai envoyés vers vous, me levant durant la nuit et les dirigeant, et que vous n’avez pas écoutés,
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
Je rendrai cette maison comme Silo, et je livrerai cette ville en malédiction à toutes les nations de la terre.
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Et les prêtres et les prophètes et tout le peuple entendirent Jérémie disant ces paroles dans la maison du Seigneur.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
Et lorsque Jérémie eut achevé de dire tout ce que le Seigneur lui avait ordonné de dire à tout le peuple, les prêtres et les prophètes et tout le peuple le saisirent, disant: Qu’il meure de mort.
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Pourquoi a-t-il prophétisé au nom du Seigneur, disant: Comme Silo, ainsi sera cette maison; et cette ville sera désolée, pour qu’il n’y ait pas d’habitant? Et tout le peuple s’assembla contre Jérémie dans la maison du Seigneur.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Et les princes de Juda entendirent ces paroles; et ils montèrent de la maison du roi dans la maison du Seigneur, et ils s’assirent à l’entrée de la porte neuve de la maison du Seigneur.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Et les prêtres et les prophètes parièrent aux princes et à tout le peuple, disant: Un jugement de mort est dû à cet homme, parce qu’il a prophétisé contre cette cité, comme vous l’avez entendu de vos oreilles.
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Et Jérémie parla à tous les princes et à tout le peuple, disant: Le Seigneur m’a envoyé, afin de prophétiser à cette maison et à cette cité toutes les choses que vous avez entendues.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Maintenant donc rendez droites vos voies et vos œuvres, et écoutez la voix du Seigneur votre Dieu; et le Seigneur se repentira du mal qu’il a annoncé contre vous.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Pour moi, voici que je suis entre vos mains; faites-moi ce qui paraît bon et juste à vos yeux;
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Mais cependant, sachez et apprenez bien que, si vous me faites mourir, vous répandrez un sang innocent contre vous et contre cette cité et ses habitants; car, en vérité, le Seigneur m’a envoyé vers vous, pour que je fisse entendre à vos oreilles toutes ces choses.
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Et les princes et tout le peuple dirent aux prêtres et aux prophètes: Un jugement de mort n’est pas dû à cet homme, parce que c’est au nom du Seigneur, notre Dieu, qu’il nous a parlé.
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Des hommes donc, d’entre les anciens du pays, se levèrent, et ils dirent à toute l’assemblée du peuple, en prenant la parole:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
Michée de Morasthie fut prophète dans les jours d’Ezéchias, roi de Juda, et parla à tout le peuple de Juda, disant: Voici ce que dit le Seigneur des armées: Sion, comme un champ, sera labourée, et Jérusalem sera réduite en un monceau de pierres, et la montagne de la maison en une haute forêt.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Est-ce qu’Ezéchias, roi de Juda, et tout Juda l’ont condamné à mort? Est-ce qu’ils ne craignirent pas le Seigneur, et ne supplièrent-ils pas la face du Seigneur, et le Seigneur ne se repentit-il pas des maux qu’il avait annoncés contre eux? C’est pourquoi nous faisons un grand mal contre nos âmes.
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
Il y eut aussi un homme prophétisant au nom du Seigneur, Urie, fils de Séméi, de Cariathiarim; et il prophétisa contre cette cité, et contre cette terre, selon toutes les paroles de Jérémie.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
Et le roi Joakim, et tous les puissants et ses princes entendirent ces paroles; et le roi chercha à le tuer. Et Urie l’apprit, et il craignit, et s’enfuit, et il entra en Egypte.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Et le roi Joakim envoya des hommes en Egypte, Elnathan, fils d’Achabor, et des hommes avec lui en Egypte.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Et ils tirèrent Urie d’Egypte, et ils l’amenèrent au roi Joakim, et il le frappa du glaive, et il jeta son cadavre dans les sépulcres des derniers du peuple.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
Donc la main d’Ahicam, fils de Saphan, fut avec Jérémie, afin qu’il ne fût pas livré aux mains du peuple, et qu’on ne le tuât pas.