< Irmiya 26 >

1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Au commencement du règne de Jéhojakim, fils de Josias, Roi de Juda, cette parole fut [adressée] à Jérémie par l'Eternel, en disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
Ainsi a dit l'Eternel: tiens-toi debout au parvis de la maison de l'Eternel, et prononce à toutes les villes de Juda qui viennent pour se prosterner dans la maison de l'Eternel, toutes les paroles que je t'ai commandé de leur prononcer; n'en retranche pas une parole.
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Peut-être qu'ils écouteront, et qu'ils se détourneront chacun de son mauvais train; et je me repentirai du mal que je pense de leur faire à cause de la malice de leurs actions.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Tu leur diras donc: ainsi a dit l'Eternel: si vous ne m'écoutez point pour marcher dans ma Loi, laquelle je vous ai proposée,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
Pour obéir aux paroles des Prophètes mes serviteurs que je vous envoie, me levant dès le matin, et [les] envoyant, lesquels vous n'avez point écoutés:
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
Je mettrai cette maison en même état que Silo, et je livrerai cette ville en malédiction à toutes les nations de la terre.
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Or les Sacrificateurs et les Prophètes, et tout le peuple entendirent Jérémie prononçant ces paroles dans la maison de l'Eternel.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
Et il arriva qu'aussitôt que Jérémie eut achevé de prononcer tout ce que l'Eternel lui avait commandé de prononcer à tout le peuple, les Sacrificateurs et les Prophètes et tout le peuple le saisirent, en disant: tu mourras de mort.
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Pourquoi as-tu prophétisé au Nom de l'Eternel, disant: cette maison sera comme Silo, et cette ville sera déserte, tellement que personne n'y habitera? Et tout le peuple s'assembla vers Jérémie dans la maison de l'Eternel.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Et les principaux de Juda ayant ouï toutes ces choses montèrent de la maison du Roi à la maison de l'Eternel, et s'assirent à l'entrée de la porte neuve de la maison de l'Eternel.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Et les Sacrificateurs et les Prophètes parlèrent aux principaux, et à tout le peuple, en disant: cet homme mérite d'être condamné à la mort, car il a prophétisé contre cette ville, comme vous l'avez entendu de vos oreilles.
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Et Jérémie parla à tous les principaux, et à tout le peuple, en disant: l'Eternel m'a envoyé pour prophétiser contre cette maison, et contre cette ville, [selon] toutes les paroles que vous avez ouïes.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Maintenant donc, corrigez votre conduite et vos actions; et écoutez la voix de l'Eternel votre Dieu, et l'Eternel se repentira du mal qu'il a prononcé contre vous.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Pour moi, me voici entre vos mains, faites de moi comme il vous semblera bon et juste.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Mais sachez comme une chose certaine, que si vous me faites mourir, vous mettrez du sang innocent sur vous, et sur cette ville, et sur ses habitants; car en vérité l'Eternel m'a envoyé vers vous, afin de prononcer toutes ces paroles, vous l'entendant.
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Alors les principaux et tout le peuple dirent aux Sacrificateurs et aux Prophètes: cet homme ne mérite pas d'être condamné à la mort; car il nous a parlé au Nom de l'Eternel notre Dieu.
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Et quelques-uns des Anciens du pays se levèrent, et parlèrent à toute l'assemblée du peuple, en disant:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
Michée Morastite a prophétisé aux jours d'Ezéchias Roi de Juda, et a parlé à tout le peuple de Juda, en disant: ainsi a dit l'Eternel des armées, Sion sera labourée [comme] un champ, et Jérusalem sera réduite en monceaux de pierres, et la montagne du Temple en de hauts lieux d'une forêt.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Ezéchias le Roi de Juda, et tous ceux de Juda le firent-ils mourir? Ne craignit-il pas l'Eternel, et ne supplia-t-il pas l'Eternel? et l'Eternel se repentit du mal qu'il avait prononcé contre eux; nous faisons donc un grand mal contre nos âmes.
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
Mais aussi, [dirent les autres], il y eut un homme qui prophétisa au Nom de l'Eternel, [savoir] Urie, fils de Sémahia, de Kiriath-jéharim, lequel ayant prophétisé contre cette même ville, et contre ce même pays, en la même manière que Jérémie;
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
Et le Roi Jéhojakim, avec tous ses officiers, et les principaux ayant entendu ses paroles, le Roi chercha à le faire mourir; mais Urie l'ayant appris, et ayant craint, s'enfuit, et se retira en Egypte.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Et le Roi Jéhojakim envoya des hommes en Egypte, [savoir] Elnathan, fils de Hacbor, et quelques gens avec lui, qui allèrent en Egypte,
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Et qui firent revenir Urie d'Egypte, et l'amenèrent au Roi Jéhojakim, qui le frappa avec l'épée, et jeta son corps mort aux sépulcres du peuple.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
Toutefois la main d'Ahikam fils de Saphan fut pour Jérémie, afin qu'on ne le livrât point entre les mains du peuple, pour le faire mourir.

< Irmiya 26 >