< Irmiya 26 >
1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Au commencement du règne de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole vint de Yahvé:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
« Yahvé dit: 'Tiens-toi dans le parvis de la maison de Yahvé, et dis à toutes les villes de Juda qui viennent se prosterner dans la maison de Yahvé toutes les paroles que je t'ordonne de leur dire. N'omets pas un mot.
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Il se peut qu'ils écoutent et que chacun revienne de sa mauvaise voie, afin que je renonce au mal que j'ai l'intention de leur faire à cause de la méchanceté de leurs actions.'"
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Tu leur diras: « Yahvé dit: 'Si vous ne m'écoutez pas, si vous ne marchez pas dans ma loi que j'ai mise devant vous,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
si vous n'écoutez pas les paroles de mes serviteurs les prophètes que je vous envoie, même en vous levant de bonne heure et en les envoyant - mais que vous n'avez pas écouté-
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
alors je rendrai cette maison semblable à Silo, et je ferai de cette ville une malédiction pour toutes les nations de la terre.'"
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Les prêtres, les prophètes et tout le peuple entendirent Jérémie prononcer ces paroles dans la maison de l'Éternel.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
Lorsque Jérémie eut achevé de dire tout ce que l'Éternel lui avait ordonné de dire à tout le peuple, les prêtres, les prophètes et tout le peuple le saisirent, en disant: « Tu mourras!
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Pourquoi as-tu prophétisé au nom de Yahvé, en disant: « Cette maison sera comme Silo, et cette ville sera déserte, sans habitant? ». Tout le peuple était entassé autour de Jérémie dans la maison de Yahvé.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Lorsque les princes de Juda eurent entendu ces choses, ils montèrent de la maison du roi à la maison de l'Éternel, et ils s'assirent à l'entrée de la nouvelle porte de la maison de l'Éternel.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Alors les prêtres et les prophètes parlèrent aux chefs et à tout le peuple, en disant: « Cet homme mérite la mort, car il a prophétisé contre cette ville, comme vous l'avez entendu de vos oreilles. »
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Alors Jérémie parla à tous les chefs et à tout le peuple, et dit: « L'Éternel m'a envoyé pour prophétiser contre cette maison et contre cette ville toutes les paroles que vous avez entendues.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Maintenant, corrigez vos voies et vos actions, et obéissez à la voix de l'Éternel, votre Dieu; alors l'Éternel se retirera du mal qu'il a prononcé contre vous.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Quant à moi, voici, je suis entre tes mains. Fais de moi ce qui est bon et juste à tes yeux.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Sachez seulement que si vous me faites mourir, vous ferez retomber le sang innocent sur vous-mêmes, sur cette ville et sur ses habitants; car en vérité, l'Éternel m'a envoyé vers vous pour prononcer toutes ces paroles à vos oreilles. »
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Alors les princes et tout le peuple dirent aux prêtres et aux prophètes: « Cet homme n'est pas digne de mourir, car il nous a parlé au nom de Yahvé notre Dieu. »
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Alors quelques-uns des anciens du pays se levèrent, et parlèrent à toute l'assemblée du peuple, en disant:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
« Michée, le Morashtite, prophétisa au temps d'Ézéchias, roi de Juda, et il parla à tout le peuple de Juda, en disant: « L'Éternel des armées dit: "'Sion sera labourée comme un champ, et Jérusalem deviendra un tas, et la montagne de la maison comme les hauts lieux d'une forêt.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Ézéchias, roi de Juda, et tout Juda ne l'ont-ils pas fait mourir? Ne craignait-il pas Yahvé, n'implorait-il pas la faveur de Yahvé, et Yahvé ne s'est-il pas détourné du malheur qu'il avait prononcé contre eux? Nous commettrions ainsi un grand mal contre nos propres âmes! ».
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
Il y avait aussi un homme qui prophétisait au nom de l'Éternel, Urie, fils de Shemahia, de Kiriath Jearim, et il prophétisa contre cette ville et contre ce pays, selon toutes les paroles de Jérémie.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
Lorsque le roi Jehoïakim, avec tous ses hommes forts et tous les princes, entendit ses paroles, le roi chercha à le faire mourir; mais Urie, l'ayant entendu, eut peur, s'enfuit et alla en Égypte.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Le roi Jehoïakim envoya en Égypte Elnathan, fils d'Acbor, et quelques hommes avec lui.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Ils allèrent chercher Urie en Égypte et l'amenèrent au roi Jojakim, qui le tua par l'épée et jeta son cadavre dans les tombes des gens du peuple.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
Mais la main d'Ahikam, fils de Shaphan, était avec Jérémie, de sorte qu'ils ne le livrèrent pas entre les mains du peuple pour le faire mourir.