< Irmiya 26 >

1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Na počátku kralování Joakima syna Joziášova, krále Judského, stalo se slovo toto od Hospodina, řkoucí:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
Takto praví Hospodin: Postav se v síňci domu Hospodinova, a mluv ke všechněm městům Judským, přicházejícím klaněti se v domě Hospodinově, všecka slova, kteráž tobě přikazuji mluviti k nim, neujímejž slova,
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
Zdali by aspoň uposlechli, a odvrátili se jeden každý od cesty své zlé, abych litoval zlého kteréž myslím učiniti jim pro nešlechetnost předsevzetí jejich.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Rciž tedy jim: Takto praví Hospodin: Neuposlechnete-li mne, abyste chodili v zákoně mém, kterýž jsem předložil vám,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
Poslouchajíce slov služebníků mých proroků, kteréž já posílám k vám, jakož jste, když jsem je, ráno přivstávaje posílal, neposlouchali:
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
Jistě žeť naložím s domem tímto jako s Sílo, a město toto vydám v proklínání všechněm národům země.
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
Slyšeli pak kněží a proroci, i všecken lid Jeremiáše mluvícího slova ta v domu Hospodinovu.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
I stalo se, že hned, jakž přestal Jeremiáš mluviti všeho, cožkoli přikázal Hospodin mluviti ke všemu lidu, jali jej ti kněží a proroci i všecken lid ten, řkouce: Smrtí umřeš.
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Proč jsi prorokoval ve jménu Hospodinovu, řka: Stane se jako Sílo domu tomuto, a město toto tak spustne, že nebude v něm žádného obyvatele? Shromažďoval se pak všecken lid k Jeremiášovi do domu Hospodinova.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
Tedy uslyšavše knížata Judská ty věci, přišli z domu královského do domu Hospodinova, a posadili se u dveří brány Hospodinovy nové.
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
I řekli kněží a proroci těm knížatům a všemu lidu, řkouce: Hoden jest smrti muž tento; nebo prorokoval proti městu tomuto, jakž jste slyšeli v své uši.
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Tedy promluvil Jeremiáš ke všechněm knížatům těm i ke všemu lidu, řka: Hospodin poslal mne, abych prorokoval o domu tomto i o městě tomto všecky ty věci, kteréž jste slyšeli.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
Protož nyní polepšte cest svých a předsevzetí svých, a poslouchejte hlasu Hospodina Boha svého, i bude litovati Hospodin toho zlého, kteréž vyřkl proti vám.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
Já pak aj, v rukou vašich jsem, učiňte mi, což se vám za dobré a spravedlivé vidí.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Ale však jistotně vězte, usmrtíte-li mne, že krev nevinnou na sebe uvedete, i na město toto, i na obyvatele jeho; nebo v pravdě poslal mne Hospodin k vám, abych mluvil v uši vaše všecka slova tato.
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
I řekli knížata i všecken lid kněžím a těm prorokům: Nemáť nikoli muž tento odsuzován býti na smrt, poněvadž ve jménu Hospodina Boha našeho mluvil nám.
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Tedy povstali někteří z starších té země, a promluvili ke všemu shromáždění lidu, řkouce:
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
Micheáš Moraštický prorokoval za času Ezechiáše krále Judského, a pravil všemu lidu Judskému, řka: Takto praví Hospodin zástupů: Sion jako pole orán bude, a Jeruzalém jako hromady, hora pak domu tohoto jako lesové vysocí.
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Zdaliž hned proto usmrtil jej Ezechiáš král Judský a všecken Juda? Zdaliž neulekl se Hospodina, a nemodlil se Hospodinu? I litoval Hospodin toho zlého, kteréž vyřkl proti nim. Protož my činíme velmi zlou věc proti dušem svým.
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
A byl také muž prorokující ve jménu Hospodinovu, Uriáš syn Semaiášův z Kariatjeharim, kterýž prorokoval o městě tomto i o zemi této v táž všecka slova jako Jeremiáš.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
A když uslyšel král Joakim a všickni udatní jeho, i všecka knížata slova jeho, hned usiloval král usmrtiti jej. O čemž uslyšev Uriáš, bál se, a utíkaje, přišel do Egypta.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Ale poslal král Joakim některé do Egypta, Elnatana syna Achborova i jiné s ním do Egypta.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
Kteříž vyvedše Uriáše z Egypta, přivedli jej k králi Joakimovi. I zabil jej mečem, a vhodil tělo jeho do hrobů lidu obecného.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
A však ruka Achikamova syna Safanova byla při Jeremiášovi, aby ho nevydával v ruku lidu k usmrcení jeho.

< Irmiya 26 >