< Irmiya 25 >
1 Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
Beseda, ki je prišla Jeremiju glede vsega Judovega ljudstva, v četrtem letu Jojakíma, Jošíjevega sina, Judovega kralja, kar je bilo prvo leto babilonskega kralja Nebukadnezarja,
2 Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
ki jo je prerok Jeremija govoril vsemu Judovemu ljudstvu in vsem prebivalcem Jeruzalema, rekoč:
3 Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
»Od trinajstega leta Jošíja, Amónovega sina, Judovega kralja, celo do današnjega dne, to je triindvajsetega leta, je prišla k meni Gospodova beseda in govoril sem vam, vzdigujoč se zgodaj in govoril; toda niste prisluhnili.
4 Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
Gospod je pošiljal k vam vse svoje služabnike preroke, vzdigujoč jih zgodaj in jih pošiljal; toda niste prisluhnil niti nagnili svojega ušesa, da bi prisluhnili.
5 Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
Rekli so: ›Sedaj se ponovno obrnite, vsakdo iz svoje zle poti in od hudobije svojih dejanj in prebivajte v deželi, ki jo je Gospod dal vam in vašim očetom na veke vekov,
6 Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
in ne hodite za drugimi bogovi, da jim služite in da jih obožujete in ne dražite me do jeze z deli svojih rok, in vam ne bom storil nobene škode.‹
7 “Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
Vendar mi niste prisluhnili, ‹ govori Gospod; ›da bi me lahko dražili do jeze z deli svojih rok v svojo lastno škodo.‹
8 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
Zato tako govori Gospod nad bojevniki: ›Ker niste poslušali mojih besed,
9 zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
glejte, poslal bom in vzel vse družine iz severa, ‹ govori Gospod ›in babilonskega kralja Nebukadnezarja, mojega služabnika in privedel jih bom zoper to deželo in zoper njene prebivalce in zoper vse te narode naokoli in popolnoma jih bom uničil in jih naredil osuplost in posmeh in neprestana opustošenja.
10 Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
Poleg tega bom od njih odvzel glas smeha in glas veselja, glas ženina in glas neveste, zvok mlinskih kamnov in svetlobo sveče.
11 Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
In ta celotna dežela bo opustošenje in osuplost; in ti narodi bodo sedemdeset let služili babilonskemu kralju.
12 “Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
Ko pa se dopolni sedemdeset let, se bo zgodilo, da bom kaznoval babilonskega kralja in ta narod, ‹ govori Gospod, ›zaradi njihove krivičnosti in deželo Kaldejcev in naredil jo bom za neprestana opustošenja.
13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
Nad to deželo bom privedel vse svoje besede, ki sem jih proglasil zoper njo, celó vse, kar je zapisano v tej knjigi, ki jo je Jeremija prerokoval zoper vse narode.
14 Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
Kajti tudi številni narodi in veliki kralji izmed njih jim bodo služili. Poplačal jim bom glede na njihova dejanja in glede na dela njihovih lastnih rok.‹«
15 Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
Kajti tako mi govori Gospod, Izraelov Bog: »Vzemi vinsko čašo te razjarjenosti pri moji roki in vsem narodom, h katerim te pošiljam, povzroči, da jo pijejo.
16 Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
Pili bodo in bodo omajani in zmešani zaradi meča, ki ga bom poslal mednje.‹«
17 Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
Potem sem vzel čašo pri Gospodovi roki in vsem narodom, h katerim me je Gospod poslal, sem dal, da pijejo:
18 Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
namreč Jeruzalemu in Judovim mestom, njihovim kraljem in njihovim princem, da jih naredim za opustošenje, osuplost, posmeh in prekletstvo; kakor je to ta dan;
19 Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
faraonu, egiptovskemu kralju, njegovim služabnikom, njegovim princem in vsemu njegovemu ljudstvu;
20 da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
vsemu pomešanemu ljudstvu in vsem kraljem dežele Uc, vsem kraljem dežele Filistejcev, Aškelónu, Gazi, Ekrónu, preostanku iz Ašdóda,
Edómu, Moábu in Amónovim sinovom,
22 dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
vsem tirskim kraljem, vsem sidónskim kraljem in kraljem otokov, ki so onstran morja,
23 Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
Dedánu, Temáju, Buzu in vsem, ki so na skrajnih vogalih
24 dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
in vsem kraljem Arabije in vsem kraljem pomešanega ljudstva, ki prebivajo v puščavi
25 dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
in vsem kraljem v Zimríju in vsem kraljem v Elámu in vsem kraljem v Mediji
26 da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
in vsem kraljem na severu, daleč in blizu, enega z drugim in vsem kraljestvom sveta, ki so na obličju zemlje; in kralj Šešáha bo pil za njimi.
27 “Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
Zatorej jim boš rekel: »Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: ›Pijte, bodite pijani, bljuvajte, padite in ne vstanite več zaradi meča, ki ga bom poslal med vas.
28 Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
In zgodilo se bo, če odklonijo vzeti čašo iz tvoje roke, da pijejo, potem jim boš rekel: ›Tako govori Gospod nad bojevniki: ›Zagotovo boste pili.‹
29 Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Kajti, glejte, začenjam prinašati zlo na mesto, ki je imenovano z mojim imenom in ali naj bi bili vi popolnoma nekaznovani? Ne boste nekaznovani, kajti poklical bom meč nad vse prebivalce zemlje, ‹ govori Gospod nad bojevniki.
30 “Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
Zato prerokuj zoper njih vse te besede in jim reci: › Gospod bo rjovel iz višine in izustil svoj glas iz svojega svetega prebivališča; mogočno bo rjovel nad svojim prebivališčem; zavpil bo kakor tisti, ki tlači grozdje, zoper vse prebivalce zemlje.
31 Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
Hrup bo prišel celó do koncev zemlje, kajti Gospod ima pravdo z narodi, pravdal se bo z vsem mesom; te, ki so zlobni, bo izročil meču, ‹ govori Gospod.
32 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
Tako govori Gospod nad bojevniki: ›Glej, zlo bo šlo naprej od naroda do naroda in od zemeljskih obal se bo dvignil velik vrtinčast veter.
33 A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
Umorjeni od Gospoda bodo na ta dan od enega konca zemlje do drugega konca zemlje. Ne bodo objokovani niti zbrani niti pokopani; za gnoj bodo na tleh.
34 Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
Tulite pastirji in jokajte; valjajte se v pepelu vodje tropa, kajti dnevi vašega klanja in vaših razpršenosti so dovršeni; padli boste kakor prijetna posoda.
35 Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
Pastirji ne bodo imeli nobene poti, da bežijo niti glavni od tropa, da pobegnejo.
36 Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
Slišati bo glas vpitja pastirjev in tuljenje vodje tropa, kajti Gospod je oplenil njihov pašnik.
37 Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
Miroljubna prebivališča so posekana zaradi Gospodove krute jeze.
38 Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.
Zapustil je svoje skrivališče kakor lev, kajti njihova dežela je zapuščena zaradi okrutnosti zatiralca in zaradi njegove krute jeze.‹«