< Irmiya 25 >
1 Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
La parole qui vint à Jérémie touchant tout le peuple de Juda, la quatrième année de Jehoïakim, fils de Josias, roi de Juda, (qui est la première année de Nebucadretsar, roi de Babylone, )
2 Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
[et] que Jérémie le prophète dit à tout le peuple de Juda, et à tous les habitants de Jérusalem, disant:
3 Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
Depuis la treizième année de Josias, fils d’Amon, roi de Juda, jusqu’à ce jour, ces 23 ans, la parole de l’Éternel m’est venue, et je vous ai parlé, me levant de bonne heure et parlant; et vous n’avez pas écouté.
4 Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
Et l’Éternel vous a envoyé tous ses serviteurs les prophètes, se levant de bonne heure et [les] envoyant; et vous n’avez pas écouté, et vous n’avez point incliné vos oreilles pour écouter,
5 Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
lorsqu’ils disaient: Revenez donc chacun de sa mauvaise voie, et de l’iniquité de vos actions, et vous habiterez sur la terre que l’Éternel vous a donnée, à vous et à vos pères, de siècle en siècle;
6 Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
et n’allez point après d’autres dieux pour les servir, et pour vous prosterner devant eux, et ne me provoquez pas par l’œuvre de vos mains; et je ne vous ferai pas de mal.
7 “Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
Mais vous ne m’avez pas écouté, dit l’Éternel, pour me provoquer par l’œuvre de vos mains, pour votre propre malheur.
8 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel des armées: Parce que vous n’avez pas écouté mes paroles,
9 zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
voici, j’envoie, et je prends toutes les familles du nord, dit l’Éternel, et Nebucadretsar, roi de Babylone, mon serviteur, et je les ferai venir contre ce pays, et contre ses habitants, et contre toutes ces nations à l’entour: et je les vouerai à la destruction, j’en ferai une désolation, et un objet de sifflement, et des déserts perpétuels;
10 Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
et je ferai périr du milieu d’eux la voix de l’allégresse et la voix de la joie, la voix de l’époux et la voix de l’épouse, le bruit des meules et la lumière de la lampe.
11 Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
Et tout ce pays sera un désert, une désolation; et ces nations serviront le roi de Babylone 70 ans.
12 “Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
Et il arrivera, quand [les] 70 ans seront accomplis, que je visiterai sur le roi de Babylone et sur cette nation-là leur iniquité, dit l’Éternel, et sur le pays des Chaldéens, et je le réduirai en désolations perpétuelles.
13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
Et je ferai venir sur ce pays toutes mes paroles que j’ai dites contre lui, tout ce qui est écrit dans ce livre, ce que Jérémie a prophétisé contre toutes les nations.
14 Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
Car plusieurs nations et de grands rois se serviront d’eux aussi; et je leur rendrai selon leurs actions, et selon l’œuvre de leurs mains.
15 Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
Car ainsi m’a dit l’Éternel, le Dieu d’Israël: Prends de ma main la coupe du vin de cette fureur, et tu en feras boire à toutes les nations auxquelles je t’envoie;
16 Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
et elles boiront et elles seront étourdies, et elles seront comme folles, à cause de l’épée que j’enverrai parmi elles.
17 Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
Et je pris la coupe de la main de l’Éternel, et j’en fis boire à toutes les nations auxquelles l’Éternel m’envoyait:
18 Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
à Jérusalem, et aux villes de Juda, et à ses rois, et à ses princes, pour les livrer à l’aridité, à la désolation, au sifflement, et à la malédiction, comme [il paraît] aujourd’hui;
19 Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
au Pharaon, roi d’Égypte, et à ses serviteurs, et à ses princes, et à tout son peuple;
20 da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
et à tout le peuple mélangé, et à tous les rois du pays d’Uts, et à tous les rois du pays des Philistins, et à Askalon, et à Gaza, et à Ékron, et au reste d’Asdod;
à Édom, et à Moab, et aux fils d’Ammon;
22 dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
et à tous les rois de Tyr, et à tous les rois de Sidon; et aux rois des îles qui sont au-delà de la mer;
23 Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
à Dedan, et à Théma, et à Buz, et à tous ceux qui coupent les coins [de leur barbe];
24 dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
et à tous les rois d’Arabie, et à tous les rois du peuple mélangé, qui demeurent dans le désert;
25 dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
et à tous les rois de Zimri, et à tous les rois d’Élam, et à tous les rois de Médie;
26 da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
et à tous les rois du nord, à ceux qui sont près et à ceux qui sont éloignés, aux uns et aux autres, et à tous les royaumes de la terre qui sont sur la face du sol; et le roi de Shéshac boira après eux.
27 “Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
Et tu leur diras: Ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Buvez et soyez ivres, et vomissez, et tombez, et vous ne vous relèverez pas devant l’épée que j’envoie parmi vous.
28 Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
Et il arrivera que, s’ils refusent de prendre la coupe de ta main pour boire, alors tu leur diras: Ainsi dit l’Éternel des armées: Certainement, vous en boirez.
29 Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Car voici, par la ville qui est appelée de mon nom, je commence à faire du mal, et vous, vous resteriez entièrement impunis? Vous ne resterez pas impunis; car j’appelle l’épée sur tous les habitants de la terre, dit l’Éternel des armées.
30 “Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
Et toi, prophétise-leur toutes ces paroles, et dis-leur: L’Éternel rugira d’en haut, et de sa demeure sainte il fera entendre sa voix; il rugira, il rugira contre son habitation, il poussera un cri contre tous les habitants de la terre, comme ceux qui foulent au pressoir.
31 Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
Le son éclatant en viendra jusqu’au bout de la terre; car l’Éternel a un débat avec les nations, il entre en jugement avec toute chair. Les méchants, il les livrera à l’épée, dit l’Éternel.
32 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
Ainsi dit l’Éternel des armées: Voici, le mal s’en ira de nation à nation, et une grande tempête se lèvera des extrémités de la terre.
33 A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
Et les tués de l’Éternel, en ce jour-là, seront depuis un bout de la terre jusqu’à l’autre bout de la terre. On ne se lamentera pas sur eux, et ils ne seront pas recueillis, et ne seront pas enterrés; ils seront du fumier sur la face du sol.
34 Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
Vous, pasteurs, hurlez et criez; et vous, les nobles du troupeau, roulez-vous par terre, car vos jours sont accomplis, pour vous tuer; et je vous disperserai, et vous tomberez comme un vase d’agrément.
35 Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
Et [tout] refuge a péri pour les pasteurs, et la délivrance, pour les nobles du troupeau.
36 Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
Il y aura une voix du cri des pasteurs et un hurlement des nobles du troupeau; car l’Éternel dévaste leur pâturage,
37 Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
et les parcs paisibles sont désolés devant l’ardeur de la colère de l’Éternel.
38 Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.
Il a abandonné son tabernacle comme un jeune lion [son fourré]; car leur pays sera une désolation devant l’ardeur de l’oppresseur et devant l’ardeur de sa colère.