< Irmiya 25 >
1 Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
Riječ upućena Jeremiji o svem narodu judejskom, četvrte godine Jojakima, sina kralja judejskog - to je prve godine Nabukodonozora, kralja babilonskog.
2 Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
Prorok
3 Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
Od trinaeste godine Jošije, sina Amonova, kralja judejskoga, sve do dana današnjeg, ove dvadeset i tri godine, dolazila mi je riječ Jahvina i ja sam vam jednako govorio, ali me niste slušali.
4 Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
I Jahve je svejednako slao k vama sve sluge svoje, proroke, ali vi niste slušali i niste prignuli uši svoje da čujete.
5 Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
I govorahu vam: “Vratite se svaki sa zla puta svojega i od zlih djela svojih i ostanite u zemlji koju Jahve dade vama i ocima vašim za sva vremena;
6 Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
i ne idite za tuđim bogovima da im služite i da im se klanjate; i ne gnjevite me djelima ruku svojih, pa vam neću ništa nažao učiniti.
7 “Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
Ali me niste poslušali - riječ je Jahvina - nego me razgnjeviste djelima ruku svojih, na svoju nesreću!”
8 Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
Zato ovako govori Jahve nad Vojskama: “Jer niste poslušali mojih riječi,
9 zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
evo, ja ću poslati i podignuti sve narode sa sjevera - riječ je Jahvina - i slugu svoga Nabukodonozora, kralja babilonskoga, i dovest ću ih na ovu zemlju i na njene stanovnike i na sve okolne narode; izručit ću ih kletom uništenju i učinit ću ih užasom i ruglom, vječnim razvalinama.
10 Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
I ugušit ću među njima svaki glas radosti i veselja, klicanje zaručnika i zaručnice i klopot žrvnja i svjetlost svjetiljke.
11 Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
Sva će se zemlja pretvoriti u pustoš i pustinju i svi će narodi služiti kralju babilonskom sedamdeset godina.
12 “Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
Ali kad se navrši sedamdeset godina, kaznit ću kralja babilonskog i narod onaj - riječ je Jahvina - za bezakonje njihovo i zemlju kaldejsku i pretvorit ću ih u vječne razvaline.
13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
Dovest ću na tu zemlju sve što sam protiv nje rekao - sve je to napisano u ovoj knjizi, što prorokova Jeremija za sve narode.”
14 Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
“I oni će služiti mnogim narodima i velikim kraljevima i platit ću im po njihovim činima i po djelima ruku njihovih.”
15 Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
Ovako mi reče Jahve, Bog Izraelov: “Uzmi ovaj pehar vina iz moje ruke i napoji njime sve narode kojima ću te poslati.
16 Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
Neka piju dok ne zateturaju i dok se ne izbezume zbog mača što ću ga među njih poslati.”
17 Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
I uzeh pehar iz ruke Jahvine i napojih njime sve narode kojima me Jahve bijaše poslao:
18 Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
Jeruzalem i gradove judejske s njihovim kraljevima i knezovima, neka budu razvalina, pustoš, ruglo i prokletstvo, kao što su i danas;
19 Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
faraona, kralja egipatskoga, s njegovim slugama i knezovima i narodom njegovim
20 da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
i svu onu mješavinu naroda: sve kraljeve zemlje Usa, sve kraljeve zemlje filistejske, Aškelon, Gazu, Ekron i ono što ostade od Ašdoda;
Edom, Moab i sinove Amonove;
22 dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
sve kraljeve Tira, sve kraljeve Sidona, kraljeve otoka onkraj mora;
23 Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
Dedan, Temu, Buz i sve one ostriženih zalizaka,
24 dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
sve kraljeve Arabije, sve kraljeve mješavine naroda koji obitavaju u pustinji;
25 dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
sve kraljeve Zimrija, sve kraljeve Elama i sve kraljeve Medije;
26 da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
sve kraljeve Sjevera, blize i daleke, jednog za drugim, i sva kraljevstva na licu zemlje. A kralj Šešak pit će poslije njih.
27 “Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
I reci im: “Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov: 'Pijte! Opijte se! Bljujte! Padnite da se više ne dignete od mača koji ću pustiti među vas.'
28 Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
Ako ne bi htjeli uzeti pehar iz tvoje ruke da piju, reci im: 'Ovako govori Jahve nad Vojskama: Morate piti!
29 Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Jer, evo, ja sam počeo kažnjavati grad koji se zove mojim imenom. A vi zar da prođete bez kazne? Ne, nećete ostati nekažnjeni, jer ću sam dozvati mač da udari na sve stanovnike zemlje' - riječ je Jahve nad Vojskama.
30 “Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
Ti im, dakle, prorokuj sve riječi ove i reci im: 'Jahve reče sa visine, iz svetoga stana grmi glasom, riče iza glasa protiv pašnjaka svoga, podvikuje kao oni što grožđe gaze. Do svih stanovnika zemlje
31 Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
dopire bojni klik - do nakraj svijeta - jer Jahve se parbi s narodima, izlazi na sud sa svakim tijelom, bezbožnike će maču izručiti - riječ je Jahvina.
32 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
Ovako govori Jahve nad Vojskama: Evo, nesreća već zahvaća narod za narodom; nevrijeme strašno već se prolama s krajeva zemlje.'”
33 A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
U onaj dan bit će pobijenih Jahvinih s jednoga kraja svijeta do drugoga. Za njima nitko neće naricati, niti će ih tko pokupiti i sahraniti; ostat će kao gnoj po zemlji.
34 Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
Kukajte, pastiri, i vičite, valjajte se po prašini, vodiči stada, jer vam se ispuniše dani za klanje, popadat ćete ko ovnovi izabrani.
35 Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
Više nema utočišta pastirima, niti spasa vodičima stada.
36 Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
Čuj, kako vapiju pastiri, kako kukaju vodiči stada, jer Jahve pustoši pašnjak njihov,
37 Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
mirna su pasišta poharana od jarosna gnjeva Jahvina.
38 Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.
Lav ostavlja guštaru jer će zemlja njihova opustjeti od mača pustošničkog, od jarosnog gnjeva Jahvina.