< Irmiya 24 >

1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
Si, Herren viste mig två fikonakorgar, satta inför Herrans tempel, sedan NebucadNezar, Konungen i Babel, hade bortfört Jechonia, Jojakims son, Juda Konung, samt med Juda Förstar, timbermän och smeder, ifrå Jerusalem, och låtit dem komma till Babel.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
Uti dem ena korgenom voro ganska god fikon, såsom de först mogna fikonen äro; uti dem andra korgenom voro ganska ond fikon, så att man intet kunde äta dem, så ond voro de.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
Och Herren sade till mig: Jeremia, hvad ser du? Jag sade: Fikon; de goda fikonen äro ganska god, och de onda äro fast ond, så att man intet kan äta dem, så ond äro de.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Då skedde Herrans ord till mig, och sade:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
Detta säger Herren, Israels Gud: Likasom dessa fikonen äro god, alltså skall jag nådeliga upptaga de fångar af Juda, hvilka jag hafver låtit hädanfara in uti de Chaldeers land;
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
Och skall nådeliga se till dem, och skall låta dem komma hit i landet igen, och skall uppbygga dem, och icke nederslå; jag skall plantera dem, och icke upprycka;
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
Och skall gifva dem hjerta till att känna mig, att jag är Herren, och de skola vara mitt folk, och jag vill vara deras Gud; ty de skola af allt hjerta vända sig till mig.
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
Men lika som de onda fikon så ond äro, att man dem icke äta kan, säger Herren; alltså vill jag bortgifva Zedekia, Juda Konung, samt med hans Förstar, och hvad qvart blifvet är i Jerusalem; de som äro qvarblefne i detta landet, och de som uti Egypti land bo.
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
Jag skall foga dem olycko till, och icke låta dem blifva i något rike på jordene, så att de skola komma till skam, till ett ordspråk, till en fabel, och till bannor, i all rum, dit jag dem bortdrifvandes varder;
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
Och skall sända svärd, hunger och pestilentie ibland dem, tilldess de skola förgås af landena, som jag dem och deras fäder gifvit hafver.

< Irmiya 24 >