< Irmiya 24 >

1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
Le Seigneur me fit voir, et voici deux paniers pleins de figues, placés devant le temple du Seigneur, après que Nabuchodonosor, roi de Babylone, eut transféré Jéchonias, fils de Joakim, roi de Juda, et ses princes, et l’artisan, et le lapidaire, loin de Jérusalem, et qu’il les eut emmenés à Babylone.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
L’un de ces paniers contenait des figues très bonnes, comme ont coutume d’être les figues de la première saison, et l’autre panier contenait des figues très mauvaises, qu’on ne pouvait manger, parce qu’elles étaient mauvaises.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
Et le Seigneur me dit: Que vois-tu, Jérémie? Et je dis: Je vois des figues bonnes, très bonnes; et des mauvaises, très mauvaises, qui ne peuvent être mangées, parce qu’elles sont mauvaises.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
Voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël: Comme ces figues sont bonnes, ainsi je traiterai bien les fils de la transmigration que j’ai envoyés de ce lieu dans la terre des Chaldéens.
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
Et je porterai sur eux un regard favorable, et je les ramènerai dans cette terre; je les rétablirai, et je ne les détruirai pas; je les planterai, et je ne les arracherai pas.
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
Et je leur donnerai un cœur, afin qu’ils me connaissent, parce que moi je suis le Seigneur; et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu, parce qu’ils reviendront à moi en tout leur cœur.
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
Quant à ces figues très mauvaises, qui ne peuvent être mangées, parce qu’elles sont mauvaises, voici ce que dit le Seigneur: Ainsi je traiterai Sédécias, roi de Juda, et ses princes, et les restes de Jérusalem qui sont demeurés dans cette ville, et ceux qui habitent dans la terre d’Egypte.
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
Je les livrerai en vexation et en affliction, dans tous les royaumes de la terre; en opprobre et en parabole, et en proverbe, et en malédiction dans tous les lieux dans lesquels je les aurai jetés.
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
Et j’enverrai contre eux le glaive, et la famine, et la peste, jusqu’à ce qu’ils soient exterminés de la terre que je leur ai donnée, à eux et à leurs pères.

< Irmiya 24 >