< Irmiya 24 >
1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
L'Éternel me fit voir que deux corbeilles de figues étaient placées devant le temple de l'Éternel, après que Nebucadnetsar, roi de Babylone, eut emmené captifs de Jérusalem Jeconia, fils de Jojakim, roi de Juda, et les princes de Juda, avec les artisans et les forgerons, et les eut emmenés à Babylone.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
L'un des paniers contenait de très bonnes figues, comme les figues de première maturité, et l'autre panier contenait de très mauvaises figues, qui ne pouvaient pas être mangées tant elles étaient mauvaises.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
Alors Yahvé me demanda: « Que vois-tu, Jérémie? » J'ai dit: « Des figues. Les bonnes figues sont très bonnes, et les mauvaises sont très mauvaises, si mauvaises qu'on ne peut pas les manger. »
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée, en ces termes:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
L'Éternel, le Dieu d'Israël, dit: « Comme ces bonnes figues, je considère comme bons les captifs de Juda que j'ai envoyés de ce lieu au pays des Chaldéens.
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
Car je les regarderai comme un bien, et je les ramènerai dans ce pays. Je les bâtirai, et je ne les abattrai pas. Je les planterai, et je ne les arracherai pas.
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
Je leur donnerai le cœur de me connaître, de savoir que je suis Yahvé. Ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu, car ils reviendront à moi de tout leur cœur.
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
"'Comme les figues mauvaises qui ne se mangent pas, tant elles sont mauvaises, dit Yahvé, je livrerai Sédécias, roi de Juda, et ses princes, et le reste de Jérusalem qui demeure dans ce pays, et ceux qui habitent au pays d'Égypte.
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
Je les livrerai même pour qu'ils soient ballottés parmi tous les royaumes de la terre, pour qu'ils soient un opprobre et un proverbe, une raillerie et une malédiction, dans tous les lieux où je les chasserai.
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
J'enverrai parmi eux l'épée, la famine et la peste, jusqu'à ce qu'ils soient exterminés du pays que j'ai donné à eux et à leurs pères.'"