< Irmiya 24 >

1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
[The army of] King Nebuchadnezzar of Babylon captured Jehoiachin, the king of Judah, and his officials, and all his skilled workers [DOU] and took them to Babylon. After that happened, Yahweh gave me a vision. [In the vision] I saw two baskets of figs that had been placed in front of the temple.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
One basket was full of good figs, like the kind that ripen first. The other basket was filled with figs that were bad/rotten, with the result that they could not be eaten.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
Then Yahweh said to me, “Jeremiah, what do you see?” I replied, “[I see some] figs. Some are very good ones, but some are very bad, with the result that no one would eat them.”
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then Yahweh gave me this message:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
“This is what [I], Yahweh, the God whom the Israeli people [say that they worship], say: ‘The good figs represent [SIM] the people of Judah whom I exiled to Babylonia.
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
I [SYN] will (watch over/take care of) them well, and [some day] I will bring them back here [to Judah]. I will establish them and cause them to be strong. I will cause them to be prosperous [MET], and I will not exile them [again].
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
I will enable them to desire to know [IDM] that I am Yahweh. They will be my people, and I will be their God, because they will return to me sincerely.’
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
But [I], Yahweh, [also] say, ‘The bad figs represent [SIM] Zedekiah, the king of Judah, and his officials, and all the [other] people who remain in Jerusalem, and those who have gone to Egypt. I will do to them like people do to rotten figs.
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
I will [get rid of them], with the result that people in every nation on the earth will be horrified, and will hate them because they are evil people. Wherever I scatter them, people will make fun of them, and say that they are disgraced, and ridicule them, and curse them.
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
And I will cause them to experience wars and famines and diseases, until they have disappeared from this land which I gave to them and to their ancestors.’”

< Irmiya 24 >