< Irmiya 24 >
1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
HERREN lod mig skue et Syn, og se, der var to Kurve Figener, som stod foran HERRENS Tempel; det var, efter at Kong Nebukadrezar af Babel havde bortført Jojakims Søn, Kong Jekonja af Juda, og Judas Fyrster, Kunsthaandværkerne og Smedene fra Jerusalem til Babel.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
Den ene Kurv indeholdt saare gode Figener, saa gode som tidligmodne, den anden saare slette Figener, saa slette, at de ikke kunde spises.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
Og HERREN sagde til mig: »Hvad ser du, Jeremias?« Jeg svarede: »Figener! De gode er saare gode og de slette saare slette, saa slette, at de ikke kan spises.«
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Da kom HERRENS Ord til mig saaledes:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
Saa siger HERREN, Israels Gud: Som man ser paa disse gode Figener, vil jeg se paa de bortførte Judæere, som jeg drev bort fra dette Sted til Kaldæernes Land.
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
Jeg vil fæste mine Øjne paa dem med Velbehag og føre dem hjem til dette Land. Jeg vil opbygge og ikke nedbryde dem, plante og ikke oprykke dem.
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
Jeg giver dem Hjerte til at kende mig, at jeg er HERREN; de skal være mit Folk, og jeg vil være deres Gud, naar de omvender sig til mig af hele deres Hjerte.
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
Men som man gør med de slette Figener, for slette til at spises, vil jeg, saa siger HERREN, gøre med Kong Zedekias af Juda og hans Fyrster og Resten af Jerusalem, dem, der er levnet i dette Land, og dem, der bor i Ægypten;
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
jeg gør dem til Rædsel for alle Jordens Riger, til Spot og Mundheld, til Haan og til et Forbandelsens Tegn paa alle de Steder, hvorhen jeg bortstøder dem;
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
jeg sender Sværd, Hunger og Pest imod dem, indtil de er udryddet af det Land, jeg gav dem og deres Fædre.