< Irmiya 24 >

1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
Jahve mi pokaza, i gle: dvije kotarice smokava stajahu pred Domom Jahvinim, pošto Nabukodonozor, kralj babilonski, odvede iz Jeruzalema i izagna u Babilon Jekoniju, sina Jojakimova, kralja judejskoga, zajedno s knezovima judejskim, kovačima i bravarima.
2 Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
U jednoj kotarici bijahu izvrsne smokve, kakve već jesu rane smokve; a u drugoj bijahu pokvarene smokve, tako rđave da se ne mogahu jesti.
3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
I Jahve me upita: “Jeremija, što vidiš?” A ja odgovorih: “Smokve! Dobre su vrlo dobre, a loše su vrlo loše - tako loše da nisu za jelo.”
4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I dođe mi riječ Jahvina:
5 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
Ovako govori Jahve, Bog Izraelov: “Kao na ove dobre smokve, tako ću milostivo pogledati na sužnje judejske koje sam s ovoga mjesta prognao u zemlju kaldejsku.
6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
I milostivo ću svrnuti oči na njih i vratiti ih u ovu zemlju. Ponovo ću ih podići i neću ih više uništiti; opet ću ih posaditi i neću ih više iščupati.
7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
I dat ću im srce da me poznaju da sam ja Jahve, da budu narod moj, a ja Bog njihov, jer će se oni svim srcem svojim opet k meni obratiti.
8 “‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
Ali kao s lošim smokvama koje su tako loše da nisu za jelo - da, riječ je Jahvina - tako ću postupiti i sa Sidkijom, kraljem judejskim, s njegovim knezovima i sa svim Jeruzalemcima što preostadoše u ovoj zemlji i s onima što se u Egiptu nastaniše.
9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
Učinit ću da budu na užas svim kraljevstvima zemaljskim, na sramotu i porugu, na ruglo i kletvu posvuda kamo ih protjeram.
10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”
I poslat ću na njih mač, glad i kugu dok se ne istrijebe sa zemlje koju dadoh njima i ocima njihovim.”

< Irmiya 24 >