< Irmiya 23 >
1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
“Otlağımın koyunlarını yok edip dağıtan çobanların vay başına!” diyor RAB.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
Halkımı güden çobanlar için İsrail'in Tanrısı RAB şöyle diyor: “Sürümü dağıtıp sürdünüz, onlarla ilgilenmediniz. Şimdi ben sizinle ilgileneceğim, yaptığınız kötülük yüzünden sizi cezalandıracağım.” RAB böyle diyor.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
“Sürmüş olduğum bütün ülkelerden sürümün sağ kalanlarını toplayıp otlaklarına geri getireceğim; orada verimli olup çoğalacaklar.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
Onları güdecek çobanlar koyacağım başlarına. Bundan böyle korkmayacak, yılgınlığa düşmeyecekler. Bir tanesi bile eksilmeyecek” diyor RAB.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
“İşte Davut için doğru bir dal Çıkaracağım günler geliyor” diyor RAB. “Bu kral bilgece egemenlik sürecek, Ülkede adil ve doğru olanı yapacak.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
Onun döneminde Yahuda kurtulacak, İsrail güvenlik içinde yaşayacak. O, ‘Yahve sidkenu’ adıyla anılacak.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
“Artık insanların, ‘İsrail halkını Mısır'dan çıkaran RAB'bin varlığı hakkı için’ demeyecekleri günler geliyor” diyor RAB.
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
“Bunun yerine, ‘İsrail soyunu kuzey ülkesinden ve sürdüğü bütün öbür ülkelerden geri getiren RAB'bin varlığı hakkı için’ diyecekler. Böylece kendi topraklarında yaşayacaklar.”
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
Peygamberlere gelince, Yüreğim paramparça, Bütün kemiklerim titriyor. RAB'bin yüzünden, O'nun kutsal sözleri yüzünden Sarhoş gibi, Şaraba yenik düşen bir adam gibiyim.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
Çünkü ülke zina edenlerle dolu, Lanet yüzünden yas tutuyor. Otlaklar kurumuş. İzledikleri yol kötü, Güçlerini haksızca kullanıyorlar.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
“Peygamber de kâhin de tanrısız; Tapınağımda bile kötülüklerini gördüm” diyor RAB.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
“Bu yüzden izledikleri yol Onlar için kaygan olacak; Karanlığa sürülecek, Orada tökezleyip düşecekler. Çünkü cezalandırılacakları yıl Başlarına felaket getireceğim” diyor RAB.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
“Samiriye peygamberleri arasında Şu iğrençliği gördüm: Baal adına peygamberlik ederek Halkım İsrail'i baştan çıkarıyorlar.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
Yeruşalim peygamberleri arasında Şu korkunç şeyi gördüm: Zina ediyorlar, yalan peşindeler. Kötülük edenleri güçlendirdiklerinden, Kimse kötülüğünden dönmüyor. Benim için hepsi Sodom gibi, Yeruşalim halkı Gomora gibi oldu.”
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
Bu nedenle Her Şeye Egemen RAB peygamberler için şöyle diyor: “Onlara pelinotu yedirecek, Zehirli su içireceğim. Çünkü Yeruşalim peygamberleri Tanrısızlığın bütün ülkeye yayılmasına neden oldular.”
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Her Şeye Egemen RAB diyor ki, “Size peygamberlik eden peygamberlerin Dediklerine kulak asmayın, Onlar sizi aldatıyor. RAB'bin ağzından çıkanları değil, Kendi hayal ettikleri görümleri anlatıyorlar.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
Beni küçümseyenlere sürekli, ‘RAB diyor ki: Size esenlik olacak!’ diyorlar. Yüreklerinin inatçılığı doğrultusunda davrananlara, ‘Başınıza felaket gelmeyecek’ diyorlar.
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
RAB'bin sözünü duyup anlamak için RAB'bin meclisinde kim bulundu ki? O'nun sözüne kulak verip duyan kim?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
İşte, RAB'bin fırtınası öfkeyle kopacak, Kasırgası döne döne kötülerin başına patlayacak.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
Aklının tasarladığını tümüyle yapana dek RAB'bin öfkesi dinmeyecek. Son günlerde açıkça anlayacaksınız bunu.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
Bu peygamberleri ben göndermedim, Ama çabucak ortaya çıktılar. Onlara hiç seslenmedim, Yine de peygamberlik ettiler.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
Ama meclisimde dursalardı, Sözlerimi halkıma bildirir, Onları kötü yollarından ve davranışlarından Döndürürlerdi.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
Ben yalnızca yakındaki Tanrı mıyım? Uzaktaki Tanrı da değil miyim?” diyor RAB,
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
“Kim gizli yere saklanır da Onu görmem?” diyor RAB, “Yeri göğü doldurmuyor muyum?” diyor RAB.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
“Adımla yalancı peygamberlik edenlerin ne dediklerini duydum. ‘Bir düş gördüm! Bir düş!’ diyorlar.
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
Kafalarından uydurdukları hileleri aktaran bu yalancı peygamberler ne zamana dek sürdürecekler bunu?
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
Ataları nasıl Baal yüzünden adımı unuttuysa, onlar da birbirlerine düşlerini anlatarak halkıma adımı unutturmayı tasarlıyorlar.
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
Düşü olan peygamber düşünü anlatsın; ama sözümü alan onu sadakatle bildirsin. Buğdayın yanında saman nedir ki?” diyor RAB.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
“Benim sözüm ateş gibi değil mi? Kayaları paramparça eden balyoz gibi değil mi?” RAB böyle diyor.
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
“İşte bunun için sözlerimi birbirlerinden çalan peygamberlere karşıyım” diyor RAB.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
“Evet, kendi sözlerini söyleyip, ‘RAB böyle diyor’ diyen peygamberlere karşıyım” diyor RAB.
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
“Uydurma düşler gören peygamberlere karşıyım” diyor RAB. “Bu düşleri anlatıyor, yalanlarla, boş övünmelerle halkımı baştan çıkarıyorlar. Ben onları ne gönderdim, ne de atadım. Bu halka hiç mi hiç yararları yok” diyor RAB.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
“Halktan biri, bir peygamber ya da kâhin, ‘RAB'bin bildirisi nedir?’ diye sorarsa, ‘Ne bildirisi?’ diye karşılık vereceksin. Sizi başımdan atacağım” diyor RAB.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
“Eğer bir peygamber, kâhin ya da başka biri, ‘Bu RAB'bin bildirisidir’ derse, onu da ailesini de cezalandıracağım.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Her biriniz komşunuza ve kardeşinize, ‘RAB ne yanıt verdi?’ ya da, ‘RAB ne söyledi?’ demelisiniz.
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
Bundan böyle, ‘RAB'bin bildirisi’ lafını ağzınıza almayacaksınız. Herkesin sözü kendi bildirisi olacak. Yaşayan Tanrı'nın, Her Şeye Egemen RAB'bin, Tanrımız'ın sözlerini çarpıtıyorsunuz siz.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Bir peygambere, ‘RAB sana ne yanıt verdi?’ ya da, ‘RAB ne söyledi?’ demelisiniz.
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
Ama, ‘RAB'bin bildirisidir’ derseniz, RAB diyor ki, ‘RAB'bin bildirisidir’ diyorsunuz. Oysa, ‘RAB'bin bildirisidir’ demeyeceksiniz diye sizi uyarmıştım.
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
Bu yüzden sizi büsbütün unutacağım, sizi de size ve atalarınıza verdiğim kenti de önümden söküp atacağım.
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
Sizi hiç unutulmayacak bir utanca düşürecek, sürekli alay konusu edeceğim.”