< Irmiya 23 >

1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
Ve eder, herdar, I som förderfven och förskingren min fosterhjord, säger Herren.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
Derföre säger Herren, Israels Gud, om de herdar, som mitt folk regera: I hafven förskingrat min hjord, och bortdrifvit, och icke besökt honom; si, jag skall hemsöka eder, för edart onda väsendes skull, säger Herren.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
Och jag skall församla, det qvart är af minom hjord, utur all land, dit jag dem utdrifvit hafver, och skall hafva dem hem igen till deras hus, att de skola växa och förökas.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
Och jag skall sätta herdar öfver dem, som dem sköta skola, att de icke mer skola frukta sig eller förskräckas, eller hemsökte varda, säger Herren.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
Si, den tiden kommer, säger Herren, att jag skall uppväcka David rättfärdighetenes frukt; och det skall vara en Konung, den väl regera skall, och skall upprätta rätt och rättfärdighet på jordene.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
På den tiden skall Juda hulpen varda, och Israel säker bo; och detta skall vara hans namn, det man honom kalla skall: Herren vår rättfärdighet.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
Derföre, si, den tid skall komma, säger Herren, då man nu intet mer skall säga: Så sant som Herren lefver, som Israels barn utur Egypti land fört hafver;
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
Utan: Så sant som Herren lefver, som Israels hus säd utförde, och hade af nordlanden, och utur all land, dit jag dem fördrifvit hafver, så att de skola nu bo i sitt land.
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
Emot Propheterna: Mitt hjerta vill mig brista i mino lifve, all min ben darra; mig är lika som enom drucknom manne, och lika som enom den af vin ragar, för Herranom, och för hans heliga ordom;
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
Att landet så fullt med horkarlar är, att landet så jämmerliga står, att det så förbannadt är, och ängarna i öknene förtorkas; och deras lefverne är ondt, och deras regemente doger intet.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
Ty både Propheter och Prester äro skalkar; och jag finner också deras ondska i mino huse, säger Herren.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
Derföre är deras väg lika som en slipper väg i mörkrena, der de uppå falla; ty Jag skall låta komma olycko öfver dem, deras hemsökningsår, säger Herren.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
Med de Propheter i Samarien hafver jag sett galenskap, att de propheterade i Baal och förförde mitt folk Israel;
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
Men med de Propheter i Jerusalem ser jag en styggelse; huru de bedrifva hor, och fara med lögn, och styrka de onda, på det att ju ingen skall omvända sig af sine ondsko. De äro alle för mig lika som Sodoma, och dess inbyggare lika som Gomorra.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
Derföre säger Herren Zebaoth om Propheterna alltså: Si, jag skall spisa dem med malört, och gifva dem galla dricka; ty ifrå Propheterna i Jerusalem kommer ut skrymteri öfver hela landet.
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Detta säger Herren Zebaoth: Hörer intet Propheternas ord, de eder prophetera; de bedraga eder, ty de predika sins hjertas syner, och icke utaf Herrans mun.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
De säga dem som mig försmäda: Herren hafver det sagt: Eder varder väl gångandes; och allom dem som vandra efter sins hjertas tycko, säga de: Det kommer ingen olycka öfver eder.
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
Ty ho hafver varit i Herrans råd, den hans ord sett och hört hafver? Ho hafver förmärkt och hört hans ord?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Si, ett Herrans väder skall komma med grymhet, och ett förskräckeligit oväder falla de ogudaktiga öfver hufvudet.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
Och Herrans vrede skall icke upphålla, tilldess han gör och uträttar det han i sinnet hafver. Härefter skolen I väl förvarat.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
Jag sände intet Propheterna, likväl lupo de; jag talade intet med dem, likväl propheterade de.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
Ty om de hade blifvit vid mitt råd och hade predikat mino folke min ord, så hade de omvändt dem ifrå deras onda väsende, och ifrå deras onda lefverne.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
Är jag icke en Gud, den hardt när är, säger Herren, och icke en Gud, den fjerran är?
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
Menar du, att någor kan så hemliga fördölja sig, att jag icke kan se honom? säger Herren. Är icke jag den som uppfyller himmel och jord? säger Herren.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
Jag hörer väl, att Propheterna predika, och prophetera lögn i mitt Namn, och säga: Mig hafver drömt, mig hafver drömt.
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
När vilja nu Propheterna igenvända? de der lögn prophetera, och prophetera sins hjertas bedrägeri;
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
Och vilja, att mitt folk skall förgäta mitt Namn, för deras drömmars skull, som den ene för den andra predikar, såsom deras fäder förgåto mitt Namn för Baals skull.
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
En Prophet, som drömmar hafver, han predike drömmar; men den som mitt ord hafver, han predike mitt ord rätt. Huru när kommer agnar och hvete tillhopa? säger Herren.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
Är icke mitt ord lika som en eld, säger Herren, och såsom en hammar, den berg sönderslår?
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Derföre, si: Jag vill till de Propheter, säger Herren, som min ord stjäla den ene dem andra.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Si, jag vill till de Propheter, säger Herren, som sitt eget ord föra, och säga: Han hafver det sagt.
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Si, jag vill till de som falska drömmar prophetera, säger Herren, och predika dem, och förföra mitt folk med sine lögn och lösaktig ting; efter jag dock intet hafver sändt dem, och intet befallt dem, och de ej heller desso folkena nyttige äro, säger Herren.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
Om detta folk, eller en Prophet, eller en Prest varder dig frågandes, och säger: Hvilket är Herrans tunge? så skall du säga till dem, hvad den tungen är: Jag skall bortkasta eder, säger Herren.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
Och om en Prophet, eller Prest, eller folk varder sägandes: Det är Herrans tunge; densamma skall jag hemsöka, och hans hus dertill.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Men så skall den ene tala med dem andra, och säga sig emellan: Hvad svarar Herren? Och hvad säger Herren?
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
Och kaller det icke mer Herrans tunga; ty hvarjom och enom skall hans egen ord vara till en tunga, efter I alltså lefvandes Guds, Herrans Zebaoths, vårs Guds ord förvänden.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Derföre skolen I säga till Propheten alltså: Hvad svarar Herren dig? Och hvad säger Herren?
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
Nu medan I sägen Herrans tunge, derföre säger Herren alltså: Efter I kallen ordet Herrans tunga, och jag till eder sändt hafver, och hafver säga låtit, att I icke skullen kallat Herrans tunga;
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
Si, så skall jag taga eder bort, och bortkasta eder samt med stadenom, som jag eder och edra fäder gifvit hafver, ifrå mitt ansigte;
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
Och skall foga eder en evig skam till, och en evig försmädelse, den aldrig förgäten skall varda.

< Irmiya 23 >