< Irmiya 23 >

1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
Ak vai, jums, gani, kas Manas ganības avis nomaitājat un izklīdinājāt, saka Tas Kungs.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
Tādēļ tā saka Tas Kungs, Israēla Dievs, par tiem ganiem, kas Manus ļaudis gana: Jūs Manas avis esat izklīdinājuši un tās esat izdzinuši un par tām neesiet zinājuši. Redzi! Es jūs piemeklēšu jūsu ļauno darbu dēļ, saka Tas Kungs.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
Un Es pats sapulcināšu Savas atlikušās avis no visām zemēm, kurp tās esmu izdzinis, un tās atkal atvedīšu uz viņu ganībām, un tās būs auglīgas un vairosies.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
Un Es pār tām iecelšu ganus, kas tās ganīs, un tās vairs nebīsies, nedz baiļosies, nedz taps piemeklētas, saka Tas Kungs.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
Redzi, nāks dienas, saka Tas Kungs, kad Es Dāvidam uzcelšu taisnības Atvasi, un Tas valdīs kā ķēniņš, un Viņam labi izdosies, un Viņš darīs tiesu un taisnību virs zemes.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
Viņa laikā Jūda taps atpestīts un Israēls dzīvos droši. Un tas būs Viņa vārds, ar ko Viņš taps nosaukts: Tas Kungs mūsu taisnība.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
Tāpēc redzi, nāks dienas, saka Tas Kungs, ka vairs nesacīs: “Tik tiešām ka Tas Kungs dzīvo, kas Israēla bērnus izvedis no Ēģiptes zemes“,
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
Bet: „Tik tiešām, ka Tas Kungs dzīvo, kas Israēla nama dzimumu izvedis un atvedis no tās zemes pret ziemeļa pusi, un no visām zemēm, kurp Es to biju aizdzinis“, jo tie dzīvos savā zemē.
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
Par tiem praviešiem mana sirds iekš manis ir salauzta, visi mani kauli dreb, es esmu kā piedzēris vīrs un kā vīrs, ko vīns pārvarējis Tā Kunga priekšā un priekš Viņa svētiem vārdiem.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
Jo zeme ir pilna laulības pārkāpēju, jo zeme bēdājās lāstu dēļ tuksneša ganības izkalst, tādēļ ka viņu ceļš ir ļauns, un viņu vara netaisna.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
Jo tā pravietis kā priesteris ir nesvēti, pat Savā namā Es atrodu viņu blēdību, saka Tas Kungs.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
Tāpēc viņu ceļš būs kā slidenums tumsībā, tur piedauzīsies un kritīs. Jo Es vedīšu pār tiem nelaimi viņu piemeklēšanas gadā, saka Tas Kungs.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
Pie tiem praviešiem Samarijā Es gan redzēju ģeķību, jo tie sludināja caur Baālu un pievīla Manus Israēla ļaudis.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
Bet pie tiem praviešiem Jeruzālemē Es redzu negantību; tie pārkāpj laulību un tinās ar viltību un stiprina ļaundarītāju rokas, ka tie neatgriežas neviens no sava ļaunuma; tie visi Man ir kā Sodoma un viņas iedzīvotāji kā Gomora.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
Tāpēc Tas Kungs Cebaot par šiem praviešiem tā saka: redzi, Es tos ēdināšu ar vērmelēm un tos dzirdināšu ar žultīm, jo no Jeruzālemes praviešiem bezkaunība izgājusi pa visu zemi.
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Tā saka Tas Kungs Cebaot: neklausiet to praviešu vārdiem, kas jums sludina; tie jūs ved nelietībā, tie runā savas sirds parādīšanu, ne no Tā Kunga mutes.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
Tie saka allažiņ uz tiem, kas Mani zaimo: Tas Kungs ir runājis, ka jums būs miers, un uz visiem, kas pēc savas sirds stūrgalvības staigā, tie saka: nelaime nenāks pār jums.
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
Jo kas bijis Tā Kunga padoma devējs? Kas viņa vārdu redzējis vai dzirdējis? Kas viņa vārdu vērā ņēmis un klausījis?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Redzi, Tā Kunga vētra celsies ar bardzību, un briesmīgs viesulis, tas gāzīsies bezdievīgiem uz galvu.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
Tā Kunga bardzība negriezīsies atpakaļ, tiekams Viņš nebūs padarījis un piepildījis Savas sirds domas; nākamās dienās jūs to gan manīsiet.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
Es nesūtīju praviešus, un tomēr tie tecēja; Es nerunāju, un tomēr tie sludināja.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
Bet ja tie būtu stāvējuši Manā padomā, tad tie Manu vārdu būtu darījuši zināmu Maniem ļaudīm un tos būtu nogriezuši no viņu ļaunā ceļa un no viņu ļauniem darbiem.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
Vai Es esmu Dievs, kas tikai ir tuvu, saka Tas Kungs, un neesmu arī Dievs, kas ir tālu?
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
Vai kas laban arī var tverties apslēptās vietās, ka Es to neredzētu? saka Tas Kungs. Vai Es nepiepildu debesis un zemi? saka Tas Kungs.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
Es to esmu dzirdējis, ko tie pravieši saka, kas Manā Vārdā sludina melus un saka: es esmu sapni redzējis, es esmu sapni redzējis.
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
Cik ilgi tas būs to praviešu sirdī, kas sludina melus un sludina savas sirds viltību,
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
Kas uz to dodas, lai Mani ļaudis Manu vārdu aizmirst caur viņu sapņiem, ko tie cits citam stāsta, kā viņu tēvi Manu vārdu aizmirsuši caur Baālu?
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
Lai tas pravietis, kas sapņus redz, sapņus stāsta, un pie kā Mans vārds ir, tas lai Manu vārdu runā patiesībā. Kāda daļa pelavām ar graudiem? saka Tas Kungs.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
Vai Mans vārds nav kā uguns, saka Tas Kungs, un kā veseris, kas sagrauž akmens kalnus?
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Tādēļ redzi, Es celšos, saka Tas Kungs, pret tiem praviešiem, kas Manus vārdus zog cits citam.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Redzi, Es celšos, saka Tas Kungs, pret tiem praviešiem, kas runā savus pašu vārdus un saka: Viņš to runājis!
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Redzi, Es celšos pret tiem, kas sludina melu sapņus, saka Tas Kungs, un tos stāsta un pieviļ Manus ļaudis ar saviem meliem un ar savām tukšām blēņām, un Es tomēr tos neesmu sūtījis un tiem nekā neesmu pavēlējis, un tie nepavisam neder šiem ļaudīm, saka Tas Kungs.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
Kad nu šie ļaudis vai kāds pravietis vai priesteris tev vaicās un sacīs: kas ir Tā Kunga nasta? Tad tev tiem būs sacīt, jūs esat tā nasta, un Es jūs gribu atmest, saka Tas Kungs.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
Un ja būs kāds pravietis, vai priesteris, vai cilvēks, kas sacīs: Tā Kunga nasta, - to vīru un viņa namu Es piemeklēšu.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Tā jums būs sacīt ikvienam uz savu tuvāku un ikvienam uz savu brāli: ko Tas Kungs atbildējis, un ko Tas Kungs runājis?
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
Bet Tā Kunga nastu jums vairs nebūs pieminēt, jo ikvienam savs vārds būs par nastu, tāpēc ka jūs esat pārgrozījuši tā dzīvā Dieva, Tā Kunga Cebaot, mūsu Dieva, vārdus.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Tā tev būs sacīt uz to pravieti: ko tev Tas Kungs atbildējis, un ko Tas Kungs runājis?
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
Bet tāpēc ka jūs sakāt: Tā Kunga nasta, tad Tas Kungs tā saka: Tāpēc ka jūs šo vārdu sakāt: Tā Kunga nasta, - kur Es taču pie jums esmu sūtījis un sacījis, jums nebūs sacīt: Tā Kunga nasta, -
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
Tādēļ, redzi, Es jūs pavisam aizmirsīšu un jūs atmetīšu no Sava vaiga, ar visu to pilsētu, ko Es jums un jūsu tēviem esmu devis.
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
Un Es pār jums celšu mūžīgu kaunu un mūžīgu negodu, ko neaizmirsīs.

< Irmiya 23 >