< Irmiya 23 >

1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
A UWE ka poe kahu i luku, a hoopuehu i ka poe hipa o ko'u kihapai! wahi a Iehova.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
Nolaila, penei ka olelo ana mai a Iehova, ke Akua o ka Iseraela, no na kahu, ka poe hanai i ko'u poe kanaka; Ua hoopuehu oukou i ka'u poe hipa, a ua kipaku ia lakou, aole i hele mai e ike ia lakou; aia hoi, e hoopai no wau maluna o oukou, i ka hewa o ka oukou hana ana, wahi a Iehova.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
A e hoiliili no wau i ke koena o ka'u poe hipa, mai na aina a pau mai, kahi a'u i hookuke aku ai ia lakou, a e hoihoi hou mai au ia lakou iloko o ko lakou mau pa: a e kawowo lakou, a mahuahua aku.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
A e hoonoho wau i kahu maluna o'lakou, he poe hanai aku ia lakou; aole lakou e makau hou, aole e weliweli, aole hoi lakou e hoopai hou ia, wahi a Iehova.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
Aia hoi, e hiki mai ana na la, wahi a Iehova, o hoala no wau no Davida, i Oha pono, i Alii e noho aupuni, a e pomaikai auanei, a e hana no oia i ka hooponopono, a i ka pololei ma ka honua.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
I kona mau la e hoolaia o ka Iuda, a e noho maluhia o ka Iseraela, a eia hoi kona inoa e kapaia mai ai, O IEHOVA KO KAKOU PONO.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
Nolaila, aia hoi, e hiki mai ana na la, wahi a Iehova, aole lakou e olelo hou mai, Ke ola la no o Iehova, ka mea nana i lawe mai ka poe mamo a Iseraela, mai ka aina o Aigupita mai;
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
Aka, Ke ola la no o Iehova, ka mea nana i lawe mai, alakai hoi i na hua o ka hale o ka Iseraela, mai ka aina o ko kukulu akau mai, a mai na aina a pau mai, kahi a'u i kipaku aku ai ia lakou; a e noho no lakou ma ko lakou aina iho.
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
Ua nahae ko'u naau iloko o'u no na kaula, haalulu no hoi ko'u mau iwi a pau. Ua like no au me ke kanaka i ona, a like hoi me ke kanaka i lanakilaia e ka waina, no Iehova, a no na huaolelo o kona Hemolele.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
No ka mea, ua piha ka aina i ka poe moekolohe; no ka mea, ke kumakena nei ka aina, no ka hoohiki ino aua: ua maloo hoi na wahi maikai o ka waonahele; ua hewa ko lakou holo ana, aole hoi i pono ko lakou ikaika.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
No ka mea, ua aia no ke kaula, a me ke kahuna, oia, ua loaa no ia'u ko lakou hewa maloko o ko'u hale, wahi a Iehova.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
Nolaila, e like auanei ko lakou aoao ia lakou, me kahi pahee maloko o ka pouli; e kipakuia'ku la no lakou, a e haule iloko olaila; no ka mea, e lawe no wau i ka hewa maluna o lakou, i ka makahiki hoi o ko lakou hoopaiia, wahi a Iehova.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
Ua ike no au i ka lapuwale maloko o na kaula o Samaria, a wanana ae lakou ma o Baala la, a alakai hewa iho la i ko'u poe kanaka, i ka Iseraela.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
Ua ike no hoi au i ka mea inoino loa iloko o na kaula o Ierusalema; moe kolohe no lakou, a hele ma ka wahahee. Hooikaika no hoi lakou i na lima o ka poe hana hewa, i hoi ole mai kekahi, mai kona hewa mai. Ua like no lakou a pau ia'u me ko Sodoma, a o ka poe hoi e noho ana malaila, ua like no me ko Gomora.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
Nolaila, penei ka olelo ana mai a Iehova o na kaua, no na kaula; Aia hoi, e hanai aku au ia lakou i ka laau awaawa, a e hoohainu aku au ia lakou i ka wai o ke au; no ka mea, mai na kaula o Ierusalema aku i hele aku ai ka aia, a i ka aina a pau.
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Ke olelo mai nei o Iehova o na kaua penei, Mai hoolohe oukou i na olelo a na kaula, ka poe wanana mai ia oukou. Hoolilo no lakou ia oukou i mea lapuwale; hai mai no lakou i ka hihio o ko lakou naau iho, aole mai ka waha o Iehova mai.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
Ke olelo ikaika mai nei lakou i ka poe hoowahawaha mai ia'u, Ua olelo mai o Iehova, E loaa ia oukou ka maluhia: a olelo no hoi lakou i kela mea i keia mea i hele mamuli o ka paakiki o kona naau iho, Aohe hewa e hiki mai ana maluna o oukou.
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
No ka mea, owai ka mea i ku ma ka ahaolelo o Iehova, a ike aku la, a lohe i kana olelo? Owai ka mea i haliu aku i kana olelo a lohe?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Aia hoi, he puahiohio no Iehova ka i puka mai me ka huhu, he puahiohio nui loa; e haule ino no ia maluna o ke poo o ka poe hewa.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
Aole e hoi hou aku ka huhu o Iehova, a hooko oia, a hana io i ka manao o kona naau. I na la mahope, e hoomaopopo loa oukou ia mea.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
Aole au i hoouna aku i keia poe kaula, ua holo nae lakou; aole au i olelo ia lakou, aka, ua wanana ae lakou.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
Aka, ina i ku lakou maloko o ka'u ahaolelo; ina ua hana aku i ko'u poe kanaka e lohe i ka'u mau olelo, ina ua hoohuli hoi lakou i kela poo, mai ko lakou aoao hewa mai, a mai ka hewa mai hoi o ka lakou hana ana.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
He Akua kokoke nei au, wahi a Iehova, aole hoi he Akua ma kahi loihi aku?
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
E huna anei kekahi ia ia iho ma na wahi malu, i ike ole aku ai au ia ia, wahi a Iehova? Aole anei au i hoopiha i ka lani, a me ka honua? wahi a Iehova.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
Ua lohe no wau i na mea a na kaula i olelo ai, ka poe i wanana wahahee ma ko'u inoa, me ka olelo iho, Ua moeuhane au, ua moeuhane au.
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
Pehea la ka loihi o ka noho ana o keia iloko o ka naau o na kaula, ka poe wanana wahahee? Oia, he poe kaula lakou no ka hoopunipuni o ko lakou naau iho;
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
He poe manao e haawi i ko'u poe kanaka i ka hoopoina i ko'u inoa, no ko lakou mau moeuhane, na mea a kela mea keia mea o lakou i hai ae i kona hoalauna, e like me ko lakou poe makua i hoopoina i ko'u inoa ma o Baala la.
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
O ke kaula moeuhane, e hai ae oia i ka moeuhane; a o ka mea ia ia ka'u olelo, e hai pololei oia i ka'u olelo. Heaha ke aa i ka palaoa, wahi a Iehova?
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
Aole anei i like ka'u olelo me ke ahi? wahi a Iehova; a like hoi me ka hamare, ka mea e nahaha ai ka pohaku?
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Nolaila au e ku e nei i na kaula, wahi a Iehova, na mea aihue i ka'u mau olelo, o kela kanaka keia kanaka i ka kona hoalauna.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Aia hoi, ke ku e nei au i na kaula, wahi a Iehova, ka poe hana me ko lakou alelo, a olelo mai, Ke i mai nei oia.
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Aia hoi, ke ku e nei au i ka poe wanana iho i na moeuhane wahahee, wahi a Iehova, a hai ae ia mau mea, a alakai hewa i ko'u poe kanaka, i ka lakou mau mea wahahee, a i ka lakou kaena ana: aole nae au i hoouna ia lakou, aole i kauoha aku ia lakou: nolaila, aole lakou e hoopomaikai iki i keia poe kanaka, wahi a Iehova.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
A hiki i ka manawa e ninau mai ai ia oe, o keia poe kanaka, a o ke kaula paha, a o ke kahuna paha, a olelo mai, Heaha ka wanana a Iehova? Alaila, e olelo aku oe ia lakou, O ka wanana hea? E haalele no wau ia oukou, wahi a Iehova.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
A o ke kaula, a o ke kahuna, a o ka lahuikanaka e olelo, Ka wanana a Iehova, na'u no e hoopai aku i kela kanaka, a me ko kona hale.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Penei oukou e olelo ai, o kela mea keia mea i kona hoalauna, o kela mea keia mea i kona hoahanau; Heaha ka Iehova i pane mai ai? a heaha hoi ka Iehova i olelo mai ai?
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
A mai hai hou oukou i ka wanana a Iehova; no ka mea, o ka olelo a kela kanaka keia kanaka, oia kana wanana: no ka mea, ua hoololi oukou i na olelo a ke Akua ola, o Iehova o na kaua, o ko kakou Akua.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Penei oe o olelo aku ai i ke kaula, Heaha ka Iehova i pane mai ai ia oe? a heaha hoi ka Iehova i olelo mai ai?
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
Aka, no ka oukou olelo ana, Ka wanana a Iehova; nolaila, penei ka olelo ana mai a Iehova; No ka oukou olelo ana mai i keia olelo, Ka wanana a Iehova, a ua hoouna aku au ia oukou, me ka i iho, Mai olelo oukou, Ka wanana a Iehova;
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
Nolaila, wau no, e hoopoina loa no wau ia oukou, a e haalele no wau ia oukou, a me ke kulanakauhale a'u i haawi aku ai ia oukou, a me ko oukou poe kupuna, a e lilo auanei oukou mai ko'u alo aku.
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
A e haawi no wau ia oukou, i mea hoowahawaha mau loa, a i hilahila pau ole, aole hoi e poinaia.

< Irmiya 23 >