< Irmiya 23 >
1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
Malheur aux pasteurs qui ruinent et dispersent les brebis de mon troupeau!" dit l’Eternel.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
C’Est pourquoi, voici ce que déclare l’Eternel, Dieu d’Israël, à l’encontre des pasteurs qui mènent mon peuple: "C’Est vous qui avez dispersé mes brebis, qui les avez fourvoyées et n’en avez pris nul soin. Eh bien, moi, j’aurai soin de vous châtier pour vos mauvaises actions, dit l’Eternel."
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
Moi, je rassemblerai les restes de mon troupeau de toutes les terres où je les ai relégués, je les ramènerai à leur pâturage, pour qu’ils y croissent et s’y multiplient.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
J’Établirai sur eux des pasteurs qui les feront paître, et ils n’auront plus de crainte, ils n’auront plus d’alarme, et il ne s’en perdra plus, dit l’Eternel.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
Voici que des jours viennent, dit l’Eternel, où je susciterai à David un rejeton juste, qui régnera en roi, agira avec sagesse et exercera le droit et la justice dans le pays.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
En ses jours, Juda sera sauf et Israël habitera en pleine sécurité, et voici le nom qu’on lui donnera: "L’Eternel est mon Droit!"
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
En vérité, des jours viendront, dit l’Eternel, où l’on ne dira plus: "Vive l’Eternel qui a fait monter les enfants d’Israël du pays d’Egypte!"
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
mais "Vive l’Eternel qui a fait monter, qui a ramené les descendants de la maison d’Israël du pays du Nord et de toutes les contrées où je les avais relégués, pour qu’ils demeurent dans leur patrie!"
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
Au sujet des prophètes: mon coeur s’est brisé en moi, tous mes membres sont frémissants, je suis comme un homme ivre, comme quelqu’un maîtrisé par le vin, à cause de l’Eternel et de ses saintes paroles.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
Car le pays est rempli de gens adultères; car par suite des parjures, le pays est en deuil, les pâturages de la campagne sont desséchés; ils se précipitent vers le mal et usent leur force pour le mensonge.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
Oui, même le prophète, même le prêtre sont infâmes; jusque dans ma maison, je constate leur perversité, dit l’Eternel.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
C’Est pourquoi la voie qu’ils suivent deviendra pour eux comme un terrain glissant en pleines ténèbres; ils seront bousculés et y tomberont, quand je ferai arriver sur eux la catastrophe, l’année de leur châtiment, dit l’Eternel.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
Aussi chez les prophètes de Samarie, j’avais vu des choses écoeurantes; ils prophétisaient au nom de Baal et égaraient mon peuple Israël.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
Mais chez les prophètes de Jérusalem j’ai remarqué des abominations: ils pratiquent l’adultère, vivent dans le mensonge, prêtent main-forte aux malfaiteurs, de façon que personne ne revienne de sa perversité. Tous, ils sont devenus à mes yeux comme gens de Sodome, et les habitants de Jérusalem comme gens de Gomorrhe.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
C’Est pourquoi, ainsi parle l’Eternel-Cebaot au sujet des prophètes: Voici, je vais leur donner des plantes vénéneuses à manger et des eaux empoisonnées à boire, car c’est des prophètes de Jérusalem que la corruption s’est propagée dans tout le pays.
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
Voici ce que dit l’Eternel-Cebaot: N’Écoutez point les discours des prophètes qui vous adressent des prophéties; ils vous bercent de chimères, ils vous débitent des visions de leur invention, que l’Eternel n’a point inspirées.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
Ils ne cessent de répéter à mes détracteurs: "L’Eternel a parlé; vous aurez la paix." Tous ceux qui suivent les penchants de leur coeur, ils leur disent: "Aucun malheur ne vous atteindra."
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
Qui donc parmi eux a assisté au conseil de l’Eternel, de manière à voir, de manière à entendre sa parole? Qui a pu tendre l’oreille à ses discours et les recueillir?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Voici, la tempête de l’Eternel éclate avec fureur, un ouragan se déchaîne, qui s’abattra sur la tête des coupables.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
La colère de l’Eternel ne cessera de sévir que quand il aura exécuté, accompli les desseins de son coeur; plus tard, vous en comprendrez le sens.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
Je n’avais point donné de mission à ces prophètes, et ils se sont mis à courir! Je ne leur avait point adressé la parole, et ils ont prophétisé!
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
S’Ils avaient assisté à mon conseil, mais alors ils auraient fait entendre mes paroles à mon peuple, ils l’auraient détourné de sa mauvaise voie et de ses mauvaises actions.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
Suis-je donc Dieu de près, dit l’Eternel, et non pas Dieu de loin?
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
Quelqu’un peut-il se cacher dans un lieu occulte, sans que je le voie? dit l’Eternel. Est-ce que je ne remplis pas le ciel et la terre? dit l’Eternel.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
J’Entends bien ce que disent les prophètes qui prophétisent faussement en mon nom, à savoir: "J’Ai eu un songe, j’ai eu un songe!"
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
Jusques à quand en sera-t-il ainsi? Entre-t-il donc dans la pensée des prophètes, prophètes de mensonge, qui débitent les perfides inventions de leur coeur,
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
entre-t-il dans leurs calculs de faire oublier mon nom à mon peuple, grâce à leurs songes qu’ils se content mutuellement, de même que leurs ancêtres ont oublié mon nom pour Baal?
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
Que le prophète qui se targue d’un songe raconte ce songe! Mais que celui qui est favorisé de ma parole annonce fidèlement ma parole: que vient faire la paille avec le grain? dit l’Eternel.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
Est-ce que ma parole ne ressemble pas au feu, dit l’Eternel, et au marteau qui fait voler en éclats le rocher?
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Aussi vais-je prendre à partie, dit l’Eternel, les prophètes qui se dérobent les uns aux autres mes révélations.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Je vais prendre à partie, dit l’Eternel, les prophètes qui font marcher leur langue et prononcent des oracles.
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Je vais prendre à partie, dit l’Eternel, les diseurs de songes trompeurs, qui les divulguent pour égarer mon peuple par leurs mensonges et leur verbiage frivole, alors que je ne leur ai donné ni mission ni ordre, et qu’ils ne peuvent rendre aucun service à ce peuple, dit l’Eternel.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
Que si ce, peuple, si prophètes ou prêtres t’interrogent en ces termes: "Quel est l’oracle de l’Eternel?" tu leur répondras ce qu’est l’oracle: "Je vais vous rejeter!" dit l’Eternel.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
Quant au prophète, au prêtre, à l’homme du peuple qui dira: "Oracle de l’Eternel", je le châtierai, cet individu, ainsi que sa maison.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Voici comme vous vous exprimerez en parlant entre vous: "Quelle réponse a faite l’Eternel? Quelle est la parole prononcée par l’Eternel?"
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
Mais le mot "oracle" de l’Eternel (Massa), vous n’en ferez plus mention; car la parole de l’Eternel communiquée à l’homme est bien un oracle (Massa), mais vous dénaturez les paroles du Dieu vivant, de l’Eternel-Cebaot, notre Dieu.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
Voici donc ce que vous pourrez dire au prophète: "Quelle réponse t’a faite l’Eternel? Quelle est la parole prononcée par l’Eternel?"
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
Mais si vous parlez de Massa de l’Eternel, assurément alors l’Eternel dira: "Puisque vous employez cette expression de Massa de l’Eternel, malgré cette défense que je vous ai fait adresser: Ne dites pas Massa de l’Eternel,
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
voici, je vais vous repousser complètement, vous rejeter, vous et la ville que j’ai donnée à vous et à vos ancêtres, de devant ma face,
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
et je ferai peser sur vous un éternel déshonneur, un opprobre permanent et inoubliable.