< Irmiya 23 >
1 “Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
What trouble is coming to the shepherds who destroy and scatter the sheep of my pasture! declares the Lord.
2 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
This is what the Lord, the God of Israel, says about the shepherds who were meant to look after my people: You have scattered my flock. You have chased them away You didn't take care of them, so now I will take care of you for all the evil you've done, declares the Lord.
3 “Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
I myself will gather what's left of my flock from all the countries where I exiled them, and I will bring them back to their pasture, where they will increase in number.
4 Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
I will put shepherds in charge of them who will take care of them, and they won't be afraid or discouraged anymore, and none of them will be missing, declares the Lord.
5 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
Look, the time is coming, declares the Lord, when I will choose a descendant of David who does what is right. As king he will rule with wisdom and do what is just and right throughout the country.
6 A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
When he is king, Judah will be saved, and Israel will live in safety. This is the name he will be called: The Lord Who Makes Us Right.
7 “Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
Look, the time is coming, declares the Lord, when people won't say anymore, “On the Lord's life, who led the Israelites out of Egypt.”
8 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
Instead they'll say, “On the Lord's life, who led the Israelites back from the northern country and all the other countries where he had exiled them.” Then they'll live in their own country.
9 Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
When it comes to the prophets: I'm really disturbed—I'm shaking inside! I stagger like a drunk, like someone who's had too much wine, because of what the Lord is like, because of his holy words.
10 Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
For the country is full of people committing adultery so it's under a curse. The land mourns and the desert pastures have dried up. The people live evil lives, using their energy to do wrong.
11 “Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
Both prophets and priests show no respect for me. I see wickedness even in my Temple, declares the Lord.
12 “Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
That's why their path will become slippery; they will be chased away in the dark and fall down. I'm going to bring disaster on them at the time when they're punished, declares the Lord.
13 “A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
I saw the prophets of Samaria doing something really offensive: They prophesied in the name of Baal and led my people Israel to sin.
14 A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
But now I see the prophets of Jerusalem doing something even more disgusting: They commit adultery and their lives are a lie. They support the wicked, so no one stops sinning. To me they're all like Sodom; the people of Jerusalem are like Gomorrah.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
So this is what the Lord Almighty says about the prophets: I will give them wormwood to eat and poisoned water to drink, because evil has spread across the country from the prophets of Jerusalem.
16 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
This is what the Lord Almighty says: Don't pay attention to what these prophets say when they prophesy to you. They're fooling you with visions they make up in their own minds. They're not from me.
17 Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
They keep on telling people who don't respect me, “The Lord says that you'll live in peace,” and to everyone following their own stubborn attitude, “Nothing bad is going to happen to you.”
18 Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
But who of them has attended the Lord's council to hear and understand what he's saying? Who has paid attention to his instructions and followed them?
19 Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
Watch out! The Lord has sent out a furious storm, a tornado swirling around the heads of the wicked.
20 Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
The Lord's anger won't fade until he's finished doing everything he wants. Only then will you really understand.
21 Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
I didn't send these prophets, but they run to deliver their messages. I didn't tell them to say anything, but they still go on prophesying.
22 Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
Now if they had attended my council, they would have delivered my instructions to my people and brought them back from their evil way of life, from their evil actions.
23 “Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
Am I only a local God and not a God who operates widely? asks the Lord.
24 Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
Can people hide in secret places where I can't see them? asks the Lord. Don't I operate everywhere in heaven and on earth? asks the Lord.
25 “Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
I've listened to the prophets who prophesy lies in my name. They say, “I've had a dream! I've had a dream!”
26 Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
How long will this continue? How long will these prophets go on prophesying these lies which are just the product of their own deluded minds?
27 Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
They think the dreams that they repeat to one another will lead my people to forget me, just like their forefathers forgot me by worshiping Baal.
28 Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
A prophet who has a dream should say it's just a dream, but anyone I've spoken to should deliver my message faithfully. What is straw in comparison to grain? asks the Lord.
29 “Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
Doesn't my word burn like fire? asks the Lord. Isn't it like a hammer smashing a rock?
30 “Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
Pay attention to this, declares the Lord. I'm opposed to those prophets who steal words from one another and then say it's a message from me.
31 I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
Pay attention to this declares the Lord. I'm opposed to those prophets who make up their own stories and then announce, “This is what the Lord says.”
32 Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
Pay attention to this declares the Lord, I'm opposed to those who prophesy fictional dreams. They tell them in order to lead my people into sin with their wild lies. I didn't send them or give them any instructions, and they don't do anybody any good, declares the Lord.
33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
So when a prophet or priest or anyone else comes and asks you, “What is ‘the burden of the Lord?’” tell them, I'm not giving you a burden. I'm giving up on you, declares the Lord.
34 In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
If a prophet or priest or anyone else claims, “This is the burden of the Lord,” I will punish that person and their family.
35 Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
This is what everybody should say to their friends and relatives: “What answer has the Lord given?” or, “What has the Lord said?”
36 Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
Don't talk about “the burden of the Lord” anymore, because everybody has different ideas about this “burden,” perverting the words of the living God, the Lord Almighty, our God.
37 Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
This is what you are to say ask any prophet: “What message has the Lord given you?” and “What has the Lord told you?”
38 Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
If they say, “This is the burden of the Lord,” then this is the Lord's response: Because you said, “This is the burden of the Lord,” and I warned you not to,
39 Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
now I'm going to pick you up like a burden and throw you away, you and the city that I gave to you and your forefathers.
40 Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”
I will disgrace you forever, you shame will never be forgotten.