< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Så sa Herren: Gå ned til Judas konges hus og tal der dette ord:
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
Hør Herrens ord, du Judas konge som sitter på Davids trone, du selv og dine tjenere og ditt folk, I som går inn gjennem disse porter!
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Så sier Herren: Gjør rett og rettferdighet, fri den plyndrede ut av undertrykkerens hånd, og gjør ikke urett og vold mot den fremmede, den farløse og enken, og utøs ikke uskyldig blod på dette sted!
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
For dersom I gjør efter dette ord, så skal konger som sitter på Davids trone, dra inn gjennem portene til dette hus på vogner og hester, kongen selv og hans tjenere og hans folk.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
Men dersom I ikke hører på disse ord, da sverger jeg ved mig selv, sier Herren, at dette hus skal bli ødelagt.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
For så sier Herren om Judas konges hus: Et Gilead er du for mig, en Libanons topp; men sannelig, jeg vil gjøre dig til en ørken, til byer som ingen bor i.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
Og jeg vil innvie ødeleggere mot dig, hver med sine våben, og de skal hugge ned dine herligste sedrer og kaste dem på ilden.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
Og mange hedninger skal gå forbi denne by og si til hverandre: Hvorfor har Herren gjort så med denne store by?
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
Og de skal svare: Fordi de forlot Herrens, sin Guds pakt og tilbad andre guder og dyrket dem.
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Gråt ikke over en død og klag ikke over ham! Gråt over ham som har draget bort! For han skal ikke mere komme tilbake og se sitt fødeland.
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
For så sier Herren om Judas konge Sallum, Josias' sønn, som blev konge efter sin far Josias, og som drog bort fra dette sted: Han skal ikke mere komme tilbake hit;
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
men på det sted som de har ført ham til i fangenskap, der skal han dø, og dette land skal han ikke se mere.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Ve ham som bygger sitt hus med urettferdighet og sine saler med urett, som lar sin næste træle for intet og ikke gir ham hans lønn,
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
som sier: Jeg vil bygge mig et rummelig hus og luftige saler, og som hugger ut vinduer på det og paneler det med sedertre og maler det med rødt.
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Er du konge fordi du kappes i å bygge av sedertre? Din far - mon han ikke åt og drakk og gjorde rett og rettferdighet? Da gikk det ham vel.
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
Han hjalp den elendige og fattige til hans rett; da gikk det vel. Er ikke dette å kjenne mig? sier Herren.
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
Men dine øine og ditt hjerte er ikke rettet på annet enn på vinning og på å utøse den uskyldiges blod og på å bruke vold og undertrykkelse.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
Derfor sier Herren så om Judas konge Jojakim, Josias' sønn: De skal ikke holde sørgehøitid over ham og rope: Ve, min bror! Ve, søster! De skal ikke holde sørgehøitid over ham og rope: Ve, herre! Ve, hans herlighet!
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
Som de begraver et asen, skal han begraves; de skal slepe ham bort og slenge ham vekk langt fra Jerusalems porter.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Stig op på Libanon og skrik, og la din røst lyde i Basan og skrik fra Abarim! For alle dine elskere er knust.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
Jeg talte til dig i din trygghet; men du sa: Jeg vil ikke høre. Dette var din ferd fra din ungdom av at du ikke hørte på min røst.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
Alle dine førere skal vinden bortføre, og dine elskere må gå i fangenskap; ja, da skal du vanæres og bli til skamme for all din ondskaps skyld.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
Du som bor på Libanon, som har ditt rede i sedrene, hvor du vil stønne når smerter kommer over dig, veer som den fødende kvinnes!
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
Så sant jeg lever, sier Herren, selv om du Konja, Jojakims sønn, Judas konge, var en signetring på min høire hånd, så vilde jeg rive dig derfra.
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
Og jeg vil gi dig i deres hånd som står dig efter livet, og i deres hånd som du gruer for, i Babels konge Nebukadnesars hånd og i kaldeernes hånd.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
Og jeg vil kaste dig og din mor som fødte dig, bort til et annet land, hvor I ikke blev født, og der skal I dø.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
Men det land de stunder efter å komme tilbake til, til det skal de ikke komme tilbake.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Er han da en foraktet, knust lerkrukke, denne mann Konja, eller et kar som ingen bryr sig om? Hvorfor er de bortkastet, han og hans ætt, og slengt bort til det land de ikke kjente?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
Land! land! land! Hør Herrens ord!
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Så sier Herren: Skriv denne mann op som barnløs, som en mann som ingen lykke har i sine levedager! For ingen av hans ætt skal mere få lykke til å sitte på Davids trone og herske over Juda.

< Irmiya 22 >