< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Tā saka Tas Kungs: noej Jūda ķēniņa namā un runā tur šo vārdu
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
Un saki: klausi Tā Kunga vārdu, Jūda ķēniņ, kas sēdi Dāvida goda krēslā, tu un tavi kalpi un tavi ļaudis, visi, kas ieejat pa šiem vārtiem.
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Tā saka Tas Kungs: nesiet tiesu un taisnību un izglābiet aplaupīto no spaidītāja rokas, un neplēšat svešinieku, bāriņu, atraitni, nedariet varas darbu un neizlejat šai vietā nenoziedzīgas asinis.
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
Jo kad jūs tā darīsiet, tad pa šā nama vārtiem ieies ķēniņi, kas sēdēs uz Dāvida goda krēsla, un brauks ar ratiem un zirgiem, pats un viņa kalpi un viņa ļaudis.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
Bet ja jūs šos vārdus neklausīsiet, tad Es pie Sevis esmu zvērējis, saka Tas Kungs, ka šim namam būs palikt par posta vietu.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
Jo tā saka Tas Kungs par Jūda ķēniņa namu: tu Man esi kā Gileāda, kā Lībanus galva, bet tiešām, Es tevi darīšu par tuksnesi un tās pilsētas bez iedzīvotājiem.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
Jo Es pret tevi iecelšu postītājus, ikvienu ar saviem ieročiem; tie nocirtīs tavus labākos ciedru kokus un tos metīs ugunī.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
Tad daudz pagānu šai pilsētai ies garām un sacīs cits uz citu: kādēļ Tas Kungs šai lielai pilsētai tā darījis?
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
Un tie sacīs: tādēļ ka tie atstājuši Tā Kunga, sava Dieva, derību un zemē metušies priekš citiem dieviem un tiem kalpojuši.
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Neraudiet par nomirušo un nežēlojiet viņu; raudiet raudādami par to, kas aiziet, jo tas neatgriezīsies atpakaļ, redzēt savas dzimtenes zemi.
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
Jo tā saka Tas Kungs par Šallumu, Josijas dēlu, Jūda ķēniņu, kas valda sava tēva Josijas vietā, kas no šās vietas aizgājis: viņš vairs negriezīsies atpakaļ,
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
Bet tai vietā, kurp tie viņu aizveduši, viņš mirs un šo zemi viņš vairs neredzēs.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Vai tam, kas savu namu uztaisa ar netaisnību un savas istabas ar viltu, kas savam tuvākam liek velti strādāt, un tam nedod savu algu,
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
Kas domā: es sev uztaisīšu augstu namu un plašas istabas, un liek sev logus izcirst un ar ciedru kokiem apsegt un ar sarkanumu apsvaidīt.
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Vai tu domā valdīt, tādēļ ka tu ar ciedru kokiem greznojies? Vai tavs tēvs neēda un nedzēra un darīja tiesu un taisnību? Tad viņam labi klājās.
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
Viņš izdeva tiesu nabagam un bēdīgam, tad viņam labi klājās. Vai tas nav mani atzīt? saka Tas Kungs.
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
Bet tavas acis un tava sirds uz citu neskatās kā vien mantu krāt un nenoziedzīgas asinis izliet, apspiest un darīt varas darbu.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
Tādēļ, tā saka Tas Kungs par Jojaķimu, Josijas, Jūda ķēniņa dēlu: par to nevaidēs: vai, mans brāli! Vai, mana māsa! par to nevaidēs: vai, kungs! Vai, cienīgais.
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
Bet kā ēzeli aprok, tā viņu apraks, un viņš taps rauts un izmests tālu no Jeruzālemes vārtiem.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Kāp uz Lībanu un sauc un pacel savu balsi Basanā un brēc no Abarima, jo visi tavi mīluļi ir satriekti.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
Es runāju uz tevi, kad tev vēl labi klājās, bet tu sacīji: es neklausīšu. Tas ir tavs ceļš no pašas jaunības, ka tu Manu balsi neesi klausījis
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
Vējš aizraus visus tavus ganus, un tavi mīluļi ies cietumā; tad tu tiešām tapsi kaunā un par apsmieklu visas savas blēdības dēļ.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
Tu uz Lībanus dzīvo un ciedru kokos taisi ligzdas, kā tev klāsies, kad tev sāpes uzies, mokas, kā dzemdētājai?
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
Tik tiešām kā Es dzīvoju, saka Tas Kungs: kaut arī Kanija, Jojaķima dēls, Jūda ķēniņš, būtu pie Manas labās rokas spiežamais gredzens, tomēr Es tevi no tejienes aizraušu.
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
Un Es tevi nodošu rokā tiem, kas tavu dvēseli meklē, un tiem rokā, priekš kā vaiga tu bīsties, proti Nebukadnecera, Bābeles ķēniņa, un Kaldeju rokā.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
Un Es izmetīšu tevi un tavu māti, kas tevi dzemdējusi, uz citu zemi, kur jūs neesiet dzimuši, un tur jums būs jāmirst.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
Un tai zemē, kurp viņu dvēselei gribēsies atpakaļ griezties, turp tie neatgriezīsies.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Vai šis vīrs Kanija ir viens nieka sadauzāms pods, jeb vai viņš trauks, kas nevienam nepatīk? Kāpēc viņš un viņa dzimums atmesti uz to zemi, ko tie nepazīst?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
Ak zeme, zeme, zeme! Klausi Tā Kunga vārdu!
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Tā saka Tas Kungs: pieraksti šo vīru par neauglīgu, par vīru, kam savu mūžu labi neizdosies. Jo nevienam no viņa dzimuma labi neklāsies, kas varētu sēdēt uz Dāvida goda krēsla un turpmāk valdīt pār Jūdu.

< Irmiya 22 >