< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Ainsi a dit l'Éternel: Descends dans la maison du roi de Juda, et prononces-y cette parole.
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
Dis: Écoute la parole de l'Éternel, roi de Juda, qui es assis sur le trône de David, toi, et tes serviteurs, et ton peuple, qui entrez par ces portes.
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Ainsi a dit l'Éternel: Faites droit et justice; délivrez l'opprimé de la main de l'oppresseur; n'opprimez pas, ne violentez pas l'étranger, ni l'orphelin ni la veuve, et ne répandez point le sang innocent dans ce lieu.
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
Car si vous agissez suivant cette parole, les rois assis sur le trône de David entreront par les portes de cette maison, montés sur des chars et sur des chevaux, eux, leurs serviteurs et leur peuple.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
Mais si vous n'écoutez pas ces paroles, j'ai juré par moi-même, dit l'Éternel, que cette maison sera réduite en ruines.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
Car ainsi a dit l'Éternel touchant la maison du roi de Juda: Tu es pour moi comme un Galaad, comme le sommet du Liban; mais certainement, je ferai de toi un désert, des villes sans habitants.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
Je prépare contre toi des destructeurs, chacun avec ses armes, qui couperont et jetteront au feu l'élite de tes cèdres.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
Et plusieurs nations passeront près de cette ville, et chacun dira à son compagnon: Pourquoi l'Éternel a-t-il fait ainsi à cette grande ville?
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
Et on répondra: Parce qu'ils ont abandonné l'alliance de l'Éternel leur Dieu, et qu'ils se sont prosternés devant d'autres dieux, et les ont servis.
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Ne pleurez point celui qui est mort; ne faites point sur lui de condoléance. Mais pleurez, pleurez celui qui s'en va; car il ne reviendra plus, il ne reverra plus le pays de sa naissance!
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
Car ainsi a dit l'Éternel, sur Shallum, fils de Josias, roi de Juda, qui régnait à la place de Josias, son père, et qui est sorti de ce lieu:
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
Il n'y reviendra plus; mais il mourra dans le lieu où on l'a transporté, et il ne verra plus ce pays.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Malheur à celui qui bâtit sa maison par l'injustice, et ses étages par l'iniquité; qui se sert de son prochain sans le payer, et ne lui donne pas le salaire de son travail;
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
Qui dit: Je me bâtirai une vaste maison, et des étages bien aérés; qui s'y fait percer des fenêtres, la lambrisse de cèdre, et qui la peint de vermillon!
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Crois-tu que tu règnes, parce que tu te piques d'employer le cèdre? Ton père n'a-t-il pas mangé et bu? Il fit droit et justice; alors il prospéra.
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
Il jugea la cause de l'affligé et du pauvre; alors il prospéra. N'est-ce pas là me connaître? dit l'Éternel.
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
Mais tu n'as des yeux et un cœur que pour ta cupidité, pour répandre le sang innocent, et pour exercer l'oppression et la violence.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
C'est pourquoi, ainsi a dit l'Éternel touchant Jéhojakim, fils de Josias, roi de Juda: On ne le pleurera point, en disant: hélas, mon frère; hélas, ma sœur! On ne le plaindra point, en disant: hélas, seigneur! hélas, sa majesté!
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
Il sera enseveli de la sépulture d'un âne; il sera traîné et jeté hors des portes de Jérusalem.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Monte au Liban, et crie; élève ta voix sur le Bassan; et crie du mont Abarim! Car tous ceux qui t'aimaient sont détruits.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
Je t'ai parlé dans tes prospérités; tu as dit: Je n'écouterai pas! Tel est ton train dès ta jeunesse: tu n'as pas écouté ma voix.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
Le vent se repaîtra de tous ceux qui te paissent, et ceux qui t'aiment iront en captivité. Certainement alors tu seras honteuse et dans l'ignominie, à cause de toute ta malice.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
Toi qui habites le Liban et qui fais ton nid dans les cèdres, que tu seras à plaindre quand te surviendront les douleurs et l'angoisse, comme à la femme en travail!
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
Je suis vivant! dit l'Éternel; quand Chonia, fils de Jéhojakim, roi de Juda, serait un cachet à ma main droite, je t'arracherais de là!
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
Je te livrerai entre les mains de ceux qui cherchent ta vie, entre les mains de ceux dont la présence te fait peur, et entre les mains de Nébucadnetsar, roi de Babylone, et entre les mains des Caldéens.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
Je te jetterai, toi et ta mère qui t'a enfanté, dans cet autre pays où vous n'êtes point nés, et c'est là que vous mourrez.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
Et quant au pays où leur âme aspire à retourner, ils n'y retourneront point.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Est-il donc, ce Chonia, un vase de rebut, mis en pièces? un ustensile qui ne fait plus de plaisir? Pourquoi sont-ils jetés, lui et sa postérité, lancés dans un pays qu'ils ne connaissent pas?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
O terre, terre, terre! écoute la parole de l'Éternel.
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Ainsi a dit l'Éternel: Inscrivez cet homme comme n'ayant point d'enfants, comme un homme qui ne prospérera point dans ses jours; car de sa postérité personne ne réussira à siéger sur le trône de David, ni à dominer encore en Juda.

< Irmiya 22 >