< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Voici ce que dit l’Eternel: "Descends à la maison du roi de Juda, et là parle en ces termes;
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
tu diras: Ecoute la parole de l’Eternel, roi de Juda, qui sièges sur le trône de David, toi et tes serviteurs et ton peuple, vous tous qui entrez par ces portes.
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Voici ce que dit l’Eternel: Pratiquez la justice et l’équité, arrachez celui qu’on dépouille des mains de l’oppresseur, ne faites subir ni avanie ni violence à l’étranger, à l’orphelin et à la veuve, et ne versez point de sang innocent en ce lieu-ci.
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
Si vraiment vous agissez de cette manière, il entrera encore par les portes de cette maison des rois de la race de David, héritiers de son trône, montés sur des chars et des chevaux, entourés de leurs officiers et de leur peuple.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
Mais si vous ne tenez pas compte de ces paroles, j’en jure par moi, dit l’Eternel, cette maison deviendra une ruine.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
Voici, en effet, ce que dit l’Eternel au sujet du palais' du roi de Juda: Tu équivaux pour moi à Ghilead, au sommet du Liban! Mais, j’en jure, je te rendrai pareil à un désert, à des villes inhabitées.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
Je ferai appel contre toi à des démolisseurs, tous armés de leurs outils: ils abattront tes plus beaux cèdres et les jetteront au feu.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
Et quand, passant près de cette ville, des peuples en foule se demanderont les uns aux autres: "Pourquoi l’Eternel a-t-il traité de la sorte cette grande cité?"
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
on leur répondra: "C’Est que ses habitants ont abandonné l’alliance de l’Eternel, leur Dieu; ils se sont prosternés devant d’autres dieux, et ils les ont adorés."
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Ne pleurez pas celui qui est mort, et ne le plaignez pas! Pleurez, pleurez celui qui est parti, car il ne reviendra plus et ne reverra pas la terre qui l’a vu naître.
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
Voici en effet ce que dit l’Eternel au sujet de Challoum, le fils de Josias, roi de Juda, qui a régné à la place de son père Josias et qui a quitté ce lieu-ci: "Il n’y reviendra plus!
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
Mais il mourra là où on l’a déporté; il ne reverra plus cette terre!"
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Malheur à celui qui bâtit sa maison à l’aide de l’injustice et surélève ses appartements au prix de l’iniquité; qui fait travailler son prochain pour rien, sans lui donner de salaire;
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
qui dit: "Je me bâtirai une maison de belle taille avec des chambres hautes, bien spacieuses"; qui y perce de larges fenêtres, l’orne de lambris de cèdre et de peinture rouge.
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Penses-tu être roi parce que tu mets ton orgueil dans le cèdre? Ton père aussi mangeait et buvait, mais il pratiquait la justice et l’équité, et par là il fut heureux;
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
il faisait droit au pauvre, au malheureux, et il s’en trouvait bien. Voilà certes, ce qui s’appelle me connaître, dit l’Eternel.
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
Mais toi, tu n’as d’yeux ni de coeur que pour ton intérêt, pour verser le sang innocent, pour exercer l’oppression et la violence.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
C’Est pourquoi, voici ce que dit l’Eternel au sujet de Joïakim, fils de Josias, roi de Juda: "On ne conduira pas son deuil en s’écriant: "Hélas! mon frère! et hélas! ma soeur!" On ne conduira pas son deuil en s’écriant: "Hélas, le Maître! et hélas! Sa Majesté!"
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
C’Est la sépulture d’un âne qu’on lui donnera; on le traînera, on le jettera au loin, hors des portes de Jérusalem.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Monte sur le Liban, fille de Sion et pousse des cris; dans Basan, fais retentir ta voix, et du haut d’Abarim pousse des cris, car ils sont brisés, tous ceux qui te chérissaient.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
Je m’adressais à toi au temps de ta prospérité, mais tu disais: "Je n’écouterai point! "Telle est ton habitude depuis ta jeunesse, de ne pas écouter ma voix.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
Tous ceux qui étaient tes guides, le vent les emportera, tes amants iront en exil: oh! alors, tu auras honte et tu rougiras de tous tes méfaits.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
O toi, qui demeures sur le Liban, qui fixes ton nid sur les cèdres, comme tu seras un objet de pitié, lorsque des douleurs viendront t’assaillir, des convulsions comparables à celles d’une femme en travail!
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
Par ma vie, dit l’Eternel, quand bien même Coniahou, fils de Joïakim, roi de Juda, serait une bague à ma main droite, je t’en arracherais,
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
et je te livrerais aux mains de ceux qui en veulent à ta vie, aux mains de ceux que tu redoutes, aux mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone et aux mains des Chaldéens!
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
Et je te jetterai, toi et ta mère qui t’a enfanté, sur une terre étrangère, où vous n’êtes pas nés, et là vous mourrez.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
Quant à la terre où leur coeur aspire à revenir, ils n’y reviendront pas.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Est-il donc, cet homme, ce Coniahou, un méprisable morceau de pot cassé, un vase dont personne ne veut? Pourquoi ont-ils été enlevés, lui et sa race, et jetés dans un pays qu’ils ne connaissent pas?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
Terre, terre, terre, écoute la parole de l’Eternel:
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Ainsi dit l’Eternel: Inscrivez cet homme comme étant sans postérité, comme un malheureux qui ne réussit à rien au cours de sa vie; car nul de sa race ne parviendra à s’asseoir sur le trône de David ni à régner sur Juda.

< Irmiya 22 >