< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Thus said Jehovah: Go down to the house of the king of Judah, and there speak these words.
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
Hear the word of Jehovah, thou king of Judah, That sittest upon the throne of David, Thou, and thy servants, and thy people, Who go in and out through these gates!
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Thus saith Jehovah: Do justice and righteousness; Deliver the spoiled out of the hand of the oppressor; To the stranger, the fatherless, and the widow Do no wrong, do no violence, And shed no innocent blood in this place!
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
For if ye shall do this, Then shall there enter in through the gates of this house Kings, who shall sit upon the throne of David, Riding in chariots and upon horses, Each one with his servants and his people.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
But if ye will not hearken to these words, By myself do I swear, saith Jehovah, That this house shall become a desolation.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
For thus saith Jehovah to the house of the king of Judah: Gilead art thou to me, yea, the summit of Lebanon; Yet will I make thee a desert, As cities not inhabited.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
I will appoint against thee destroyers, Every one with his weapons; And they shall cut down thy choice cedars, And cast them into the fire.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
And many nations shall pass by this city, And they shall say one to another, “Wherefore hath Jehovah done thus to this great city?”
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
Then shall they answer: “Because they forsook the covenant of Jehovah their God, And worshipped strange gods, And served them.”
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Weep not for him that is dead, Make no lamentation for him! Weep, weep ye for him who is gone away; For he shall return no more, Nor see his native land!
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
For thus saith Jehovah Concerning Shallum, the son of Josiah, king of Judah, Who reigned instead of Josiah his father, Who went forth from this place: He shall return to it no more;
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
But in the place whither they have led him captive shall he die, And shall see this land no more.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Woe to him that buildeth his house with injustice, And his upper apartments with wrong; That exacteth a man's service without wages, And giveth him no recompense!
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
That saith, “I will build me a large house, And spacious apartments,” And that cutteth out windows, And ceileth it with cedar, And painteth it with vermilion!
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Shalt thou reign because thou rivallest others in cedar? Did not thy father eat and drink? Yet he had regard to justice and equity; Therefore it was well, with him.
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
He maintained the cause of the poor and needy; Then was it well with him; Was not this to know me, saith Jehovah?
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
But thine eyes and thy heart are only upon thine own gain, And the shedding of innocent blood, And deeds of violence and oppression.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
Therefore thus saith Jehovah, Concerning Jehoiakim, the son of Josiah, king of Judah: They shall not lament for him, saying, “Alas, my brother!” or, “Alas, sister!” They shall not lament for him, saying, “Alas, lord!” or, “Alas, his glory!”
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
With the burial of an ass shall he be buried, Dragged along and cast forth beyond the gates of Jerusalem.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Go thou up to Lebanon and cry, [[O Jerusalem!]] And upon Bashan lift up thy voice; Cry aloud from Abarim! For all thy lovers are fallen.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
I spake to thee in thy prosperity, But thou saidst, “I will not hear.” This hath been thy manner from thy youth; Thou hast not obeyed my voice.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
The wind shall consume all thy shepherds, And thy lovers shall go into captivity; Then shalt thou be ashamed And confounded for all thy wickedness.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
O thou that dwellest in Lebanon, That makest thy nest in cedars, How wretched shalt thou be, when anguish cometh upon thee, Pain, as of a woman in travail!
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
As I live, saith Jehovah, Thou Coniah, son of Jehoiakim, king of Judah, Though thou wert the signet upon my right hand, Even thence would I pluck thee!
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
And I will give thee into the hand of them that seek thy life, And into the hand of them that thou fearest, Even into the hand of Nebuchadnezzar, king of Babylon, And into the hand of the Chaldaeans.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
And I will cast thee forth, And thy mother that bore thee, Into a foreign land, Where ye were not born; And there shall ye die.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
To the land to which they desire to return, Thither shall they not return.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
“Is then this man Coniah a contemptible broken vessel? Is he a vessel which no man careth for? Wherefore are he and his offspring cast forth, And thrown into a land which they know not?”
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
O land, land, land, hear the word of Jehovah!
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Thus saith Jehovah: Write ye this man childless, A man that shall not be prosperous through his life; For none of his offspring shall prosper, So as to sit on the throne of David, And reign hereafter in Judah.

< Irmiya 22 >