< Irmiya 22 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Thus says the Lord: “Descend to the house of the king of Judah, and there you shall speak this word.
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
And you shall say: Listen to the word of the Lord, O king of Judah, who sits upon the throne of David: you and your servants, and your people, who enter through these gates.
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Thus says the Lord: Exercise judgment and justice, and free anyone who is oppressed by violence from the hand of a false accuser. And do not be willing to sadden the new arrival, or the orphan, or the widow, nor should you burden them unfairly. And you shall not shed innocent blood in this place.
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
For if you will indeed accomplish this word, then there will enter through the gates of this house kings from the stock of David, sitting on his throne, and riding on chariots and on horses: they, and their servants, and their people.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
But if you will not listen to these words, I swear by myself, says the Lord, that this house will be in desolation.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
For thus says the Lord about the house of the king of Judah: You are to me like Gilead, the head of Lebanon. Certainly, I will make you desolate, with uninhabitable cities.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
And I will sanctify over you the destroying man and his weapons. And they will cut down your select cedars and throw them violently into the fire.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
And many nations will pass through this city. And each one will say to his neighbor: ‘Why has the Lord acted in this way toward this great city?’
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
And they will answer: ‘It is because they abandoned the covenant of the Lord their God, and they adored strange gods and served them.’
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
You should not choose to weep for the dead, nor should you mourn over them with tears. Lament for him who is departing, for he will return no more, nor will he see his native land again.
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
For thus says the Lord to Shallum, the son of Josiah, the king of Judah, who reigned in place of his father, who has departed from this place: He will not return here again.
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
Instead, he will die in the place to which I have transferred him, and he will not see this land anymore.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Woe to one who builds his house with injustice and his upper rooms without judgment, who oppresses his friend without cause and does not pay him his wages.
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
And he says: ‘I will build a broad house for myself, with spacious upper rooms.’ He makes windows for himself, and he builds the roof out of cedar, and he paints it with red ocher.
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Will you reign because you compare yourself to the cedar? Did your father not eat and drink, and act with judgment and justice, so that it would be well with him?
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
He judged the case of the poor and the indigent for their good. Was this not because he knew me, says the Lord?
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
Yet truly, your eyes and your heart are toward avarice and the shedding of innocent blood, and toward false accusations and the pursuit of evil deeds.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
Because of this, thus says the Lord toward Jehoiakim, the son of Josiah, king of Judah: They will not mourn for him by saying, ‘Alas,’ to a brother, or, ‘Alas,’ to a sister. They will not make a noise for him and say, ‘Alas,’ to a master, or, ‘Alas,’ to a nobleman.
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
He will be buried with the burial of a donkey, having rotted and been thrown out of the gates of Jerusalem.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Ascend to Lebanon and cry out! And utter your voice in Bashan, and cry out to those passing by. For all your lovers have been crushed.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
I spoke to you in your abundance, and you said, ‘I will not listen.’ This has been your way from your youth, for you have not listened to my voice.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
The wind will feed all your shepherds, and your lovers will go into captivity. And then you will be confounded, and you will be ashamed of all your wickedness.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
You who sit in Lebanon, and who nest in the cedars, in what way did you mourn when suffering came to you, like the suffering of a woman giving birth?
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
As I live, says the Lord, if Jeconiah, the son of Jehoiakim, the king of Judah, were a ring on my right hand, I would remove him from there.
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
And I will deliver you into the hand of those who seek your life, and into the hand of those whose face you dread, and into the hand of Nebuchadnezzar, the king of Babylon, and into the hand of the Chaldeans.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
And I will send you, and your mother who conceived you, into a foreign land, in which you were not born, and there you shall die.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
And to the land about which they lift up their mind, thinking to return there, they shall not return.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Is this man, Jeconiah, a broken earthenware vessel? Is he a vessel which is entirely unpleasing? Why have they been cast out, he and his offspring, cast out even into a land that they have not known?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
O earth, O earth, O earth! Listen to the word of the Lord!
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Thus says the Lord: Write: this man is barren; he is a man who will not prosper in his days. For there will not be a man from among his offspring who will sit upon the throne of David, or have authority in Judah, anymore.”