< Irmiya 22 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
Така казва Господ: Слез в къщата на Юдовия цар, та изговори там това слово, като кажеш:
2 ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
Слушай словото Господно, царю Юдов, Който седиш на Давидовия престол, Ти, и слугите ти, и людете ти, Които влизате през тия порти
3 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Така казва Господ: Извършвайте правосъдие и правда, И отървавайте обрания от ръката на насилника; Не онеправдавайте, нито насилвайте Чужденеца, сирачето и вдовицата, И невинна кръв не проливайте на това място.
4 Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
Защото, ако наистина вършите това, Тогава през портите на тоя дом ще влизат Царе, седящи на Давидовия престол, Возени на колесници и яздещи коне, Те, слугите им, и людете им.
5 Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
Но ако не послушате тия думи, Заклевам ми в Себе Си, казва Господ, Че тоя дом ще запустее.
6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
Защото така казва Господ за дома на Юдовия цар: Ти Ми си Галаад и ливански връх; Но ще те обърна в пустиня, В градове ненаселени.
7 Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
Ще приготвя против тебе изтребители, Всеки с оръжията му; Та ще изсекат отбраните ти кедри И ще ги хвърлят в огъня.
8 “Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
И много народи, като минат край тоя град, Ще рекат на ближния си: Защо постъпи така Господ с тоя голям град?
9 Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
И ще отговорят: Защото оставиха завета на Господа своя Бог Та се поклониха на други богове И им служиха.
10 Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
Не плачете за умрелия, Нито ридайте за него; Но плачете горчиво за оногова, който отива, Защото няма да се върне вече, Нито ще види пак родната си земя.
11 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
Защото така казва Господ За Селума, син на Юдовия цар Иосия, Който царуваше вместо баща си Иосия, Който и излезе от това място: Той няма да се върне вече;
12 Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
Но на мястото гдето го закараха пленник, там ще умре, И няма да види вече тая земя.
13 “Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
Горко на онзи, който строи къщата си с неправда, И стаите си с кривда; Който кара ближния си да му работи без заплата, И не му дава надницата му;
14 Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
Който си казва: Ще си построя голяма къща и широки стаи, В които си отваря прозорци, И я покрива с кедър, и я боядисва с алено.
15 “Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
Понеже гледаш да си натрупаш кедрове, ще царуваш ли? Баща ти не ядеше и не пиеше ли? Да! но той извършваше правосъдие и правда, Тогава благоденствуваше.
16 Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
Отсъждаше делото на сиромаха и на немотния; Тогава благоденствуваше. Не значеше ли това да Ме познава? казва Бог.
17 “Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
А твоите очи и твоето сърце не са в друго, Освен в нечестната си печалба, и в проливане невинна кръв, И в извършване насилство и угнетение.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
Затова, така казва Господ За Юдовия цар Иоаким, Иосиевия син: Няма да го оплакват, казвайки: Горко, брате мой! или: Горко сестро! Няма да го плачат, казвайки: Горко, господарю! или: Горко, негово величество!
19 Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
Той ще бъде погребан със оселско погребение, Извлечен и хвърлен оттатък ерусалимските порти.
20 “Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
Възлез на Ливан та извикай, С висок глас извикай от Аварим към Васан, Защото загинаха всичките ти любовници.
21 Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
Говорих ти в благоденствието ти; Но ти рече: Не ща да слушам. Такава е била обходата ти от младостта ти, Че ти не слушаше гласа ми.
22 Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
Вятърът ще се храни с всичките ти овчари, И любовниците ти ще отидат в плен; Навярно тогава ще се смутиш и посрамиш Поради всичката си злина.
23 Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
Ти, която населяваш Ливан, Която правиш гнездото си в кедрите, Колко ще бъдат за жалене, Когато те нападнат мъки, Болки, като на жена, която ражда!
24 “Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
Заклевам се в живота Си, казва Господ, Че даже ако Иехония, син на Юдовия цар Иоаким, Би бил печат на дясната Ми ръка, И от там бих те откъснал;
25 Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
И ще те предам в ръката на ония, които искат живота ти, И в ръката на ония, от които се боиш, Да! в ръката на Вавилонския цар Навуходоносора, И в ръката на халдейците.
26 Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
Ще отхвърля тебе И майка ти, която те е родила, В друга земя, дето не сте се родили; И там ще умрете.
27 Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
А в земята гдето душата им желае да се върне, Там няма да се върнат.
28 Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
Нима тоя човек Иехония е строшено и презряно грънчарско изделие, Или непотребен съд? Тогава защо бяха отметнати, той и потомството му, И бяха хвърлени в страна, която не познават?
29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
О, земльо, земльо, чуй словото Господно:
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”
Така казва Господ: Запишете тоя човек за бездетен, Човек, който няма да успее в дните си; Защото ни един човек от потомството му Ще успее да седи на Давидовия престол И да властвува вече над Юда.

< Irmiya 22 >