< Irmiya 21 >

1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Dette er det ord som kom til Jeremias fra Herren da kong Sedekias sendte Pashur, Malkias sønn, og presten Sefanja, Ma'asejas sønn, til ham og lot si:
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
Spør Herren for oss! For Babels konge Nebukadnesar strider mot oss. Kanskje Herren vil gjøre med oss efter alle sine undergjerninger, så han drar bort fra oss.
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
Da sa Jeremias til dem: Så skal I si til Sedekias:
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg vender om de krigsvåben som er i eders hånd, og som I strider med utenfor muren mot Babels konge og mot kaldeerne, som har kringsatt eder, og jeg vil samle dem midt i denne by.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
Og jeg vil selv stride mot eder med utrakt hånd og med sterk arm og med vrede og harme og stor fortørnelse.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
Og jeg vil slå denne bys innbyggere, både mennesker og dyr; i en stor pest skal de dø.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Og derefter, sier Herren, vil jeg gi Sedekias, Judas konge, og hans tjenere og folket, de som i denne by er blitt igjen efter pesten, sverdet og hungersnøden, i Babels konge Nebukadnesars hånd og i deres fienders hånd og i deres hånd som står dem efter livet; og han skal slå dem med sverdets egg, han skal ikke spare dem og ikke skåne og ikke forbarme sig.
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
Og til dette folk skal du si: Så sier Herren: Se, jeg legger frem for eder livets vei og dødens vei:
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Den som blir i denne by, skal dø ved sverd og ved hunger og ved pest; men den som drar ut og går over til kaldeerne, som har kringsatt eder, skal bli i live, og han skal få sitt liv til krigsbytte.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
For jeg har vendt mitt åsyn imot denne by til det onde og ikke til det gode, sier Herren; i Babels konges hånd skal den bli gitt, og han skal brenne den op med ild.
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
Og til Judas konges hus skal du si: Hør Herrens ord, du Davids hus!
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
Så sier Herren: Hold rett hver morgen, og fri den som er plyndret, ut av undertrykkerens hånd, forat ikke min harme skal fare ut som ild og brenne uten at nogen slukker, for eders onde gjerningers skyld!
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Se, jeg kommer over dig, du som bor i dalen, på berget på sletten, sier Herren - I som sier: Hvem kan komme ned og overfalle oss, og hvem kan komme inn i våre boliger?
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
Jeg vil hjemsøke eder efter frukten av eders gjerninger, sier Herren, og jeg vil tende ild på dets skog, og den skal fortære alt rundt omkring det.

< Irmiya 21 >