< Irmiya 21 >

1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Zedekia raja Yehuda mengutus kepadaku Imam Pasyhur anak Malkia, dan Imam Zefanya anak Maaseya. Ia menyuruh mereka menyampaikan kepadaku permintaan ini,
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
"Mintalah petunjuk dari TUHAN untuk kita, sebab Nebukadnezar raja Babel dengan pasukannya sedang mengepung kota kita. Barangkali TUHAN akan mengadakan keajaiban untuk kita, dan memaksa Nebukadnezar menarik mundur pasukannya."
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
Lalu TUHAN berbicara kepadaku, maka aku menyuruh orang-orang yang diutus itu
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
memberitahukan kepada Zedekia bahwa TUHAN, Allah Israel, berkata begini, "Zedekia, Aku akan mengalahkan pasukanmu yang sedang bertempur melawan raja Babel dan pasukannya. Senjata-senjata tentaramu akan Kutumpuk di tengah-tengah kota.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
Aku sendiri akan memerangi kamu dengan sekuat tenaga dan dengan kemarahan yang meluap-luap.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
Penduduk kota ini akan Kubunuh; baik manusia maupun binatang akan mati karena wabah penyakit yang dahsyat.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Engkau dan para pegawaimu serta orang-orang yang luput dari peperangan, kelaparan dan wabah penyakit, semuanya akan Kubiarkan ditangkap oleh Raja Nebukadnezar dan oleh musuh-musuh yang mau membunuhmu. Nebukadnezar akan membunuh kamu semua tanpa ampun dan tanpa belas kasihan. Aku, TUHAN, telah berbicara."
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
Lalu TUHAN menyuruh aku berkata begini kepada umat-Nya, "Dengarkan! Aku, TUHAN, memberi kepadamu suatu pilihan: jalan yang menuju kehidupan, atau jalan yang menuju kematian.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Setiap orang yang tinggal di dalam kota akan mati karena perang, kelaparan, atau wabah penyakit. Tapi mereka yang keluar untuk menyerah kepada orang Babel yang sedang menyerang kota ini, akan luput dan tidak dibunuh.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
Aku sudah memutuskan untuk menghancurkan kota ini, dan tidak menyayangkannya. Kota ini akan diserahkan kepada raja Babel; ia akan membakarnya sampai habis sama sekali. Aku, TUHAN, telah berbicara."
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
TUHAN menyuruh aku menyampaikan pesan ini kepada keluarga raja Yehuda, keturunan Daud: "Dengarkan apa yang Aku, TUHAN, katakan. Berusahalah supaya keadilan dijalankan setiap hari. Lepaskanlah orang yang diperas dari kekuasaan orang yang memerasnya. Kalau tidak, maka kejahatan yang kaulakukan akan membuat kemarahan-Ku berkobar seperti api yang tak dapat dipadamkan."
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Kemudian TUHAN berkata kepada Yerusalem, "Hai Yerusalem! Letakmu lebih tinggi dari lembah-lembah di sekitarmu. Engkau seperti bukit batu menjulang di padang yang rata, tapi Aku akan melawan engkau. Engkau berkata bahwa tak seorang pun dapat menyerangmu atau mendobrak benteng-bentengmu,
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
tapi Aku akan menghukum engkau karena perbuatanmu. Istanamu akan Kubakar, dan segala sesuatu di sekitarnya akan terbakar juga. Aku, TUHAN, telah berbicara."

< Irmiya 21 >