< Irmiya 21 >
1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Parole qui fut adressée à Jérémie par le Seigneur, quand le roi Sédécias envoya vers lui Phassur, fils de Melchias, et Sophonias, le prêtre, fils de Maasias, disant:
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
Consulte pour nous le Seigneur, parce que Nabuchodonosor, roi de Babylone, combat contre nous; pour savoir si le Seigneur agira avec nous selon toutes ses merveilles, et si l’ennemi s’éloignera de nous.
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
Et Jérémie leur dit: Ainsi vous direz à Sédécias:
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
Voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël: Voilà que moi, j’enlèverai les instruments de guerre qui sont en vos mains, et avec lesquels vous combattez contre le roi de Babylone et contre les Chaldéens, qui vous assiègent autour des murs, et je les rassemblerai au milieu de cette cité.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
Et je combattrai moi-même contre vous avec une main étendue, et avec un bras fort, et avec fureur, et avec indignation, et avec une grande colère.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
Et je frapperai les habitants de cette cité: les hommes et les bêtes mourront d’une grande peste.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Et après cela, dit le Seigneur, je livrerai Sédécias, roi de Juda, et ses serviteurs et son peuple, et ceux qui auront été épargnés dans cette cité par la peste, et par le glaive, et par la famine, à la main de Nabuchodonosor, roi de Babylone, et à la main de leurs ennemis, et à la main de ceux qui cherchent leur âme; et il les frappera du tranchant du glaive, et on ne le fléchira pas, et il n’épargnera pas, et il n’aura pas de pitié.
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
Et à ce peuple tu diras: Voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je mets devant vous la voie de la vie et la voie de la mort.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Celui qui habitera dans cette ville mourra par le glaive, et par la famine, et par la peste; mais celui qui sortira et qui fuira chez les Chaldéens qui vous assiègent, vivra, et son âme sera pour lui comme une dépouille qu’il aura sauvée.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
Car j’ai posé ma face vers cette cité pour son mal, et non pour son bien, dit le Seigneur; elle sera livrée à la main du roi de Babylone, et il la brûlera entièrement par le feu.
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
Et tu diras à la maison du roi de Juda: Ecoutez la parole du Seigneur;
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
Maison de David, voici ce que dit le Seigneur: Rendez dès le matin la justice, et arrachez celui qui est opprimé par la violence de la main de l’oppresseur, de peur que ne sorte comme un feu mon indignation, et qu’elle ne s’enflamme, et qu’il n’y ait personne qui l’éteigne, à cause de la malice de vos œuvres.
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Voilà que moi je viens à toi, habitante de la vallée solide et de la plaine, dit le Seigneur; à vous qui dites: Qui nous frappera? et qui entrera dans nos maisons?
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
Et je vous visiterai, dit le Seigneur, selon le fruit de vos œuvres; et j’allumerai un feu dans sa forêt, et il dévorera toutes choses autour d’elle.