< Irmiya 21 >

1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Yahweh gave me another message when King Zedekiah [of Judah] sent [a man who was also named] Pashhur, the son of Malkijah, and a priest named Zephaniah, the son of Maaseiah, [to talk to me. They pleaded with me], saying,
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
“[The army of] King Nebuchadnezzar of Babylon is attacking Judah. Please speak to Yahweh for us. [Ask him if he will help us]. Perhaps he will force Nebuchadnezzar’s [army] to leave by performing a miracle for us, like the miracles he performed [previously].”
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
I replied to them, “[Go back to King] Zedekiah. Tell him,
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
‘This is what Yahweh, the God whom [we] Israelis [worship], says: “I will cause your weapons to be useless in fighting against the king of Babylon and his army that is outside the walls of Jerusalem, attacking. I will enable them to enter into the center of this city.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
I myself will fight against your [army] with my very great power, [MTY, DOU] because I am very angry with you.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
I will send a very (terrible plague/big sickness) on the people of this city, and on their domestic animals, and [many of] them will die.”
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
And Yahweh says there are many people in this city who want to kill you. So, he will enable [the army of] King Nebuchadnezzar of Babylon and other people in this city to capture [you], King Zedekiah, and your officials, and [all the other] people who do not die from the plague. His army will slaughter your soldiers; they will not act mercifully toward you(pl) or pity you at all. [DOU]’
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
And tell this to [all] the people: ‘Yahweh says that you must decide whether you want to die or to remain alive.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Everyone who remains in Jerusalem will die. They will be killed in battles or die from being hungry or from diseases. But those who surrender to the army of Babylon that is surrounding your city will remain alive. They will escape dying.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
[That will happen] because I, Yahweh, have decided to cause this city to experience disasters, not to experience something good. The army of the king of Babylon will capture this city and will destroy it [completely] by fire.’”
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
[Yahweh also told me to] say this to the family of the king of Judah: “Listen to this message from Yahweh!
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
This is what he says to you descendants of King David: ‘Every day, make fair decisions for the people whom you judge. Help those who have been robbed. Rescue/Save them from those [SYN] who (oppress them/treat them cruelly). If you do not do that, I will be angry and punish [MTY] you with a fire that will be impossible to extinguish, because of [all] the sins that you have committed.
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
I will fight against you people [of Jerusalem], you who live on top of a rocky hill above the valley. [I will fight against] you people who boast, saying, “No one can attack us and break through [our defenses].”
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
I will punish you for your wicked deeds like you deserve to be punished; [It will be as though] I will light a fire in your forests that will burn up everything around you!’”

< Irmiya 21 >