< Irmiya 21 >
1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
The word which it came to Jeremiah from with Yahweh when sent to him the king Zedekiah Pashhur [the] son of Malkijah and Zephaniah [the] son of Maaseiah the priest saying.
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
Seek please for us Yahweh for Nebuchadnezzar [the] king of Babylon [is] waging war on us perhaps he will do Yahweh with us according to all wonders his and he may go up from on us.
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
And he said Jeremiah to them thus you will say! to Zedekiah.
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
Thus he says Yahweh [the] God of Israel here I [am] about to turn round [the] weapons of war which [are] in hand your which you [are] fighting by them with [the] king of Babylon and with the Chaldeans who are laying siege on you from [the] outside of the wall and I will gather them into [the] middle of the city this.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
And I will fight I with you by a hand outstretched and by an arm strong and in anger and in rage and in wrath great.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
And I will strike down [the] inhabitants of the city this and the humankind and the animal[s] by a pestilence great they will die.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
And after thus [the] utterance of Yahweh I will give Zedekiah [the] king of Judah and servants his - and the people and those [who] remain in the city this from the pestilence - from the sword and from the famine in [the] hand of Nebuchadnezzar [the] king of Babylon and in [the] hand of enemies their and in [the] hand of [those who] seek life their and he will strike down them to [the] mouth of [the] sword not he will have mercy on them and not he will show pity and not he will have compassion.
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
And to the people this you will say thus he says Yahweh here I [am] putting before you [the] way of life and [the] way of death.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
The [one who] remains in the city this he will die by the sword and by famine and by pestilence and the [one who] goes out and he will fall on the Chaldeans who are laying siege on you (and he will live *Q(K)*) and it will belong to him life his to plunder.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
For I have set face my on the city this for harm and not for good [the] utterance of Yahweh in [the] hand of [the] king of Babylon it will be given and he will burn it with fire.
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
And to [the] house of [the] king of Judah hear [the] word of Yahweh.
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
O house of David thus he says Yahweh judge to the morning justice and deliver [one who] has been robbed from [the] hand of an oppressor lest it should go forth like fire rage my and it will burn and there not [will be one who] extinguishes because of [the] wickedness of (deeds your. *Q(K)*)
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Here I [am] against you O inhabitant of the valley O rock of the plain [the] utterance of Yahweh O those [who] say who? will he come down on us and who? will he come in hiding places our.
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
And I will visit [judgment] on you according to [the] fruit of deeds your [the] utterance of Yahweh and I will kindle a fire in forest its and it will consume all around it.