< Irmiya 21 >

1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Det Ord, som kom til Jeremias fra Herren, der Kong Zedekias sendte Paskur, Malkias's Søn, og Zefanja, Maasejas Søn, Præsten, til ham og lod sige:
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
Adspørg dog Herren for os; thi Nebukadnezar, Kongen af Babel, fører Krig imod os; maaske Herren dog vilde gøre imod os efter alle sine underlige Gerninger, saa at denne maatte drage bort fra os.
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
Og Jeremias sagde til dem: Saaledes skulle I sige til Zedekias:
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
Saa sagde Herren, Israels Gud: Se, jeg vender de Krigsvaaben, som ere i eders Hænder, og med hvilke I uden for Muren stride imod Kongen af Babel og Kaldæerne, som belejre eder, og samler dem midt i denne Stad.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
Og jeg vil stride imod eder med en udrakt Haand og med en stærk Arm, og med Vrede og med Harme og med stor Fortørnelse.
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
Og jeg vil slaa denne Stads Indbyggere, baade Menneskene og Dyrene; de skulle dø ved en stor Pest.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Og derefter, siger Herren, vil jeg give Judas Konge, Zedekias, og hans Tjenere og Folket og dem, som i denne Stad ere blevne tilovers fra Pesten, fra Sværdet og fra Hungeren, i Nebukadnezar, Kongen af Babels Haand og i deres Fjenders Haand og i deres Haand, som søge efter deres Liv; og han skal slaa dem med skarpe Sværd, han skal ikke spare dem og ikke skaane dem og ikke vise Medlidenhed.
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
Og du skal sige til dette Folk: Saa siger Herren: Se, jeg lægger for eders Ansigt Livets Vej og Dødens Vej.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Den, som bliver i denne Stad, skal dø ved Sværdet og ved Hungeren og ved Pesten: Men den, som drager ud og gaar over til Kaldæerne, som belejre eder, skal blive i Live og have sit Liv som Bytte.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
Thi jeg har vendt mit Ansigt imod denne Stad til det onde og ikke til det gode, siger Herren; den skal gives i Kongen af Babels Haand, og han skal opbrænde den med Ild.
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
Og om Judas Konges Hus hører Herrens Ord.
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
Davids Hus! saa siger Herren: Holder Ret om Morgenen, og redder den, som er bleven til Rov, af Voldsmandens Haand, paa det min Vrede ikke skal fare ud som en Ild og brænde, saa at ingen skal kunne udslukke den, for eders Idrætters Ondskabs Skyld!
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Se, jeg kommer til dig, du Beboer af Dalen, af. Klippen paa Sletten! siger Herren; I, som sige: Hvo vil stige ned til os, og hvo vil komme ind i vore Boliger?
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
Og jeg vil hjemsøge eder efter eders Idrætters Frugt, siger Herren, og antænde en Ild i dens Skov, og den skal fortære alting trindt omkring den.

< Irmiya 21 >