< Irmiya 20 >
1 Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
Torej Pašhúr, Imêrjev sin, duhovnik, ki je bil tudi glavni voditelj v Gospodovi hiši, je slišal, da je Jeremija prerokoval te stvari.
2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
Potem je Pašhúr udaril preroka Jeremija in ga vtaknil v klade, ki so bile pri Benjaminovih visokih velikih vratih, ki so bila pri Gospodovi hiši.
3 Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
Naslednji dan se je pripetilo, da je Pašhúr privedel Jeremija iz klad. Potem mu je Jeremija rekel: » Gospod tvojega imena ne imenuje Pašhúr, temveč Magor misabib.
4 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
Kajti tako govori Gospod: ›Glej, naredil te bom sebi in vsem tvojim prijateljem za strahoto. Ti bodo padli pod mečem svojih sovražnikov in tvoje oči bodo to gledale in celotnega Juda bom izročil v roko babilonskega kralja in ta jih bo odvedel ujete v Babilon in jih umoril z mečem.
5 Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
Poleg tega bom izročil vso moč tega mesta, vse njegove trude, vse njegove dragocene stvari in vse zaklade Judovih kraljev bom dal v roko njihovih sovražnikov, ki jih bodo oplenili, jih vzeli in jih odnesli v Babilon.
6 Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
Ti, Pašhúr in vsi, ki prebivate v tvoji hiši, boste šli v ujetništvo. Prišel boš v Babilon in tam boš umrl in tam boš pokopan, ti in vsi tvoji prijatelji, katerim si prerokoval laži.‹«
7 Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
Oh Gospod, zavedel si me in bil sem zaveden. Močnejši si kakor jaz in si prevladal. Vsak dan sem v posmeh, vsakdo me zasmehuje.
8 Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
Kajti odkar sem govoril, sem vpil, razglašal nasilje in plen, ker mi je bila Gospodova beseda vsak dan narejena [v] grajo in posmeh.
9 Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
Potem sem rekel: »Ne bom ga omenjal niti ne bom več govoril v njegovem imenu.« Toda njegova beseda je bila v mojem srcu kakor goreč ogenj, zaprta v mojih kosteh, jaz pa sem bil izmučen od prizanašanja in nisem mogel ostati.
10 Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
Kajti slišal sem psovanje mnogih, strah na vsaki strani. »Ovadite, « so rekli »in ovadili bomo.« Vsi moji znanci so opazovali moje oklevanje, rekoč: »Morda bo premamljen in bomo prevladali zoper njega in svoje maščevanje bomo izvedli nad njim.«
11 Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Toda Gospod je z menoj kakor mogočen strahovitež. Zato se bodo moji preganjalci spotaknili in ne bodo prevladali. Silno bodo osramočeni, kajti ne bodo uspeli. Njihova večna zmeda ne bo nikoli pozabljena.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
Toda, oh Gospod nad bojevniki, ki preizkušaš pravične in vidiš notranjosti in srce, naj vidim tvoje maščevanje na njih, kajti tebi sem odprl svojo pravdo.
13 Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
Prepevajte Gospodu, hvalite Gospoda, kajti dušo ubogega je osvobodil pred roko hudodelcev.
14 La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
Preklet bodi dan, na katerega sem bil rojen. Naj ne bo blagoslovljen dan, na katerega me je moja mati rodila.
15 La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
Preklet bodi človek, ki je prinesel novice mojemu očetu, rekoč: »Fantek se ti je rodil, « in ga tako naredil zelo veselega.
16 Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
Naj bo ta človek kakor mesta, ki jih je Gospod razdejal in se ni pokesal. Naj sliši jok zjutraj in vriskanje opoldan,
17 Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
ker me ni usmrtil od maternice; ali da bi bila moja mati moj grob in njena maternica vedno obilna z menoj.
18 Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?
Zakaj sem prišel ven iz maternice, da vidim trud in bridkost, da bi bili moji dnevi použiti s sramoto?