< Irmiya 20 >

1 Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
Kwathi uPhashuri umphristi indodana ka-Imeri, induna enkulu ethempelini likaThixo, ezwe uJeremiya ephrofitha lezizinto,
2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
wenza ukuthi uJeremiya umphrofethi atshaywe njalo wamvalela esitokisini eSangweni laPhezulu koBhenjamini ethempelini likaThixo.
3 Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
Ngosuku olwalandelayo, uPhashuri esemkhupha esitokisini, uJeremiya wathi kuye, “Ibizo lakho oliphiwe nguThixo akusiPhashuri, kodwa uMagori-Misabibi,
4 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
ngoba uThixo uthi: ‘Ngizakwenza ubelucuku ngokwakho lakubo bonke abangane bakho; uzababona ngamehlo akho besiwa ngenkemba yezitha zabo. UJuda wonke ngizamnikela enkosini yaseBhabhiloni, ezabathumba ibase eBhabhiloni loba ibabulale ngenkemba.
5 Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
Yonke inotho yedolobho leli ngizayipha izitha zabo lazozonke izithelo zalo, zonke izinto zalo eziligugu kanye lemfuyo yonke yamakhosi akoJuda zizayithumba njengempango ziyithwalele eBhabhiloni.
6 Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
Wena Phashuri, labo bonke abahlala endlini yakho lizathunjwa liye eBhabhiloni. Uzafela khonale, ungcwatshwe khonale, wena kanye labangane bakho bonke ophrofetha amanga kubo.’”
7 Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
Awu Thixo, wangiyenga, ngayengeka; wangehlula wanqoba. Ngiyahlekwa insuku zonke; bonke bayangiklolodela.
8 Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
Zonke izikhathi lapho ngikhuluma, ngiyakhala ngimemezela ukuba kube lodlakela lokuchitheka. Ngakho ilizwi likaThixo selingilethele isithuko lensolo ilanga lonke.
9 Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
Kodwa nxa ngisithi, “Kangiyikumqamba loba ngikhulume ngebizo lakhe futhi,” ilizwi lakhe lisenhliziyweni yami njengomlilo, umlilo ovalelwe emathanjeni ami. Sengidiniwe ngokuligodla ngaphakathi; impela, ngingeke nganelise.
10 Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
Ngizwa abanengi benyenyeza besithi, “Kulokuthuthumela indawo yonke! Mmangaleleni! Kasimangalele!” Abangane bami bonke balindele ukuwa kwami, besithi, “Mhlawumbe uzakhohliseka; besesimehlula siphindisele kuye.”
11 Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Kodwa uThixo ulami njengebutho elilamandla; ngakho abangihluphayo bazakuwa banganqobi. Bazakwehluleka njalo bayangeke kakhulu; ihlazo labo kaliyikukhohlakala lanini.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
Awu Thixo Somandla, wena ohlola abalungileyo, uhlole inhliziyo lengqondo, kangibone ukuphindisela kwakho kubo, ngoba indaba yami ngiyinikele kuwe.
13 Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
Hlabelani uThixo! Limdumise uThixo! Uhlenga impilo yabaswelayo ezandleni zababi.
14 La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
Kaluqalekiswe usuku engazalwa ngalo! Usuku umama angizala ngalo kalungabusiswa!
15 La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
Kaqalekiswe umuntu owayabikela ubaba izindaba, owamemeza wathaba, esithi, “Uzalelwe indodana!”
16 Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
Lowomuntu kabe njengamadolobho uThixo awachitha kungekho sihawu. Kezwe ukulila ekuseni, lomkhosi wempi emini.
17 Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
Ngoba kangibulalelanga esiswini, umama enjengengcwaba lami, isisu sakhe sikhukhumele kokuphela.
18 Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?
Ngaphumelani esiswini ukuba ngibone uhlupho losizi njalo akuthi ngiphethe insuku zami ngiphakathi kwehlazo?

< Irmiya 20 >