< Irmiya 20 >

1 Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
Alors Pashur, fils d'Immer Sacrificateur, qui était prévôt [et] conducteur dans la maison de l'Eternel, entendit Jérémie qui prophétisait ces choses.
2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
Et Pashur frappa le Prophète Jérémie, et le mit dans la prison qui est à la haute porte de Benjamin, en la maison de l'Eternel.
3 Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
Et il arriva dès le lendemain, que Pashur tira Jérémie hors de la prison, et Jérémie lui dit: l'Eternel n'a pas appelé ton Nom Pashur, mais Magor-missabib.
4 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
Car ainsi a dit l'Eternel: voici, je vais te livrer à la frayeur, toi, et tous tes amis, qui tomberont par l'épée de leurs ennemis, et tes yeux le verront; je livrerai tous ceux de Juda entre les mains du Roi de Babylone, qui les transportera à Babylone, et les frappera avec l'épée.
5 Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
Et je livrerai toutes les richesses de cette ville, et tout son travail, et tout ce qu'elle a de précieux, je livrerai, dis-je, tous les trésors des Rois de Juda, entre les mains de leurs ennemis, qui les pilleront, les enlèveront, et les emporteront à Babylone.
6 Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
Et toi, Pashur, et tous les habitants de ta maison, vous irez en captivité, tu iras à Babylone, tu y mourras, et y seras enseveli, toi et tous tes amis, auxquels tu as prophétisé le mensonge.
7 Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
Ô Eternel! tu m'as sollicité, et j'ai été attiré; tu as été plus fort que moi, et tu as eu le dessus; je suis un objet de moquerie tout le jour, chacun se moque de moi.
8 Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
Car depuis que je parle je n'ai fait que jeter des cris, que crier violence et pillerie, parce que la parole de l'Eternel m'est tournée en opprobre et en moquerie tout le jour.
9 Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
C'est pourquoi j'ai dit: je ne ferai plus mention de lui, et je ne parlerai plus en son Nom; mais il y a eu dans mon cœur [comme] un feu ardent, renfermé dans mes os; je suis las de le porter, et je n'en puis plus.
10 Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
Car j'ai ouï les insultes de plusieurs, la frayeur [m'a saisi] de tous côtés. Rapportez, [disent-ils], et nous le rapporterons. Tous ceux qui ont paix avec moi épient si je bronche, [et disent]: peut-être qu'il sera abusé; alors nous aurons le dessus, et nous nous vengerons de lui.
11 Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Mais l'Eternel est avec moi comme un homme fort et terrible; c'est pourquoi ceux qui me persécutent seront renversés, ils n'auront point le dessus, ils seront honteux; car ils n'ont pas été prudents; ce sera une confusion éternelle, [qui] ne s'oubliera jamais.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
C'est pourquoi, Eternel des armées, qui sondes les justes, qui vois les reins et le cœur, fais que je voie la vengeance que tu en feras; car je t'ai découvert ma cause.
13 Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
Chantez à l'Eternel, louez l'Eternel; car il a délivré l'âme des pauvres de la main des méchants.
14 La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
Maudit soit le jour auquel je naquis; que le jour auquel ma mère m'enfanta ne soit point béni.
15 La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
Maudit soit l'homme qui apporta de bonnes nouvelles à mon père, en lui disant: un enfant mâle t'est né; et qui le réjouit si bien.
16 Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
Que cet homme-là soit comme les villes que l'Eternel a renversées sans s'en repentir, qu'il entende le cri au matin, et le retentissement bruyant au temps du Midi.
17 Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
Que ne m'a-t-on fait mourir dans le sein de ma mère? pourquoi ma mère ne m'a-t-elle été mon sépulcre, et pourquoi son sein n'a-t-il conçu [sans] jamais enfanter.
18 Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?
Pourquoi suis-je né pour ne voir que peine et qu'ennui, et afin que mes jours fussent consumés avec honte?

< Irmiya 20 >