< Irmiya 20 >

1 Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
Og Paskur, Immers Søn, Præsten, som var Overopsynsmand i Herrens Hus, hørte Jeremias spaa disse Ord.
2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
Og Paskur slog Profeten Jeremias og lagde ham i Blokken, som var ved Benjamins øverste Port paa Herrens Hus.
3 Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
Og det skete den anden Dag, da lod Paskur Jeremias komme ud af Blokken; og Jeremias sagde til ham: Herren har ikke kaldet dit Navn Paskur, men Magor-Missabib.
4 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
Thi saa siger Herren: Se, jeg vil gøre dig til Rædsel for dig selv og for alle dine Venner, og de skulle falde for deres Fjenders Sværd, og dine Øjne skulle se det; og jeg vil give al Juda i Kongen af Babels Haand, og han skal bortføre dem til Babel og slaa dem med Sværdet.
5 Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
Og jeg vil give alt Gods i denne Stad og alt Udbytte af dens Arbejde og alle dens Kostbarheder, ja, alle Judas Kongers Skatte vil jeg give i deres Fjenders Haand, at de skulle røve dem og tage dem og føre dem til Babel.
6 Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
Og du, Paskur, og alle de, som bo i dit Hus, skulle bo i Fangenskab; og du skal komme til Babel, og der skal du dø og begraves der, du og alle dine Venner, for hvilke du har spaaet Løgn.
7 Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
Herre! du har overtalt mig, og jeg lod mig overtale, du har været mig for stærk og fik Overhaand; jeg er bleven til Latter den ganske Dag, hver Mand spotter mig.
8 Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
Thi naar jeg taler, maa jeg skrige, raabe om Vold og Mishandling; thi Herrens Ord er blevet, mig til Spot og Haan den ganske Dag.
9 Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
Vel har jeg sagt: Jeg vil ikke komme ham i Hu og ej tale mere i hans Navn; men det er blevet i mit Hjerte som en brændende Ild, der er indesluttet i mine Ben, og jeg har søgt med Møje at holde det ud; men jeg kunde ikke.
10 Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
Thi jeg har hørt manges ondskabsfulde Tale, der er Rædsel trindt omkring, de sige: Angiver! saa ville vi angive ham; alle de Mænd, som skulde holde Fred med mig, tage Vare paa, om jeg haltede, og sige: Han maatte maaske lade sig forlede, at vi kunde faa Overhaand over ham og hævne os paa ham.
11 Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Men Herren er med mig som en vældig Helt, derfor skulle mine Forfølgere snuble og ikke faa Overhaand; de skulle vorde saare beskæmmede, thi de have ikke handlet forstandigt, til en evig Skam, som ikke skal glemmes.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
Og du, Herre Zebaoth, som prøver den retfærdige, og som ser Nyrer og Hjerte! jeg skal se din Hævn paa dem; thi til dig har jeg overdraget min Sag.
13 Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
Synger for Herren, lover Herren; thi han har udfriet den elendiges Sjæl af de ondes Haand.
14 La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
Forbandet være den Dag, paa hvilken jeg blev født; den Dag, paa hvilken min Moder fødte mig, vorde ikke velsignet!
15 La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
Forbandet være den Mand, som bragte min Fader et godt Budskab og sagde: Dig er født et Drengebarn, og som glædede ham saare!
16 Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
Og den Mand skal vorde som de Stæder, hvilke Herren omstyrtede og ikke angrede det, og han skal høre Raab om Morgenen og Krigsskrig ved Middagstid,
17 Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
fordi jeg ej blev dræbt i Moders Liv, saa at min Moder blev min Grav, og hendes Liv vedblev at være frugtsommeligt evindelig.
18 Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?
Hvorfor gik jeg ud af Moders Liv for at se Møje og Sorg, og for at mine Dage skulle endes med Skam?

< Irmiya 20 >